< Salmos 119 >
1 Inmensamente felices son los de proceder intachable, Quienes andan en la Ley de Yavé.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Inmensamente felices son los que observan sus Testimonios, Los que lo buscan de todo corazón.
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 Ellos tampoco cometen injusticia. Andan en los caminos de Él.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Tú nos ordenaste Que guardemos tus Preceptos con diligencia.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 ¡Cómo anhelo que sean establecidos mis caminos, Para guardar tus Estatutos!
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Entonces no sería yo avergonzado Cuando observe todos tus Mandamientos.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 Te daré gracias con rectitud de corazón Cuando aprenda tus rectos juicios.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Guardaré tus Estatutos. No me abandones completamente.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 ¿Cómo puede un joven guardar puro su camino? Al mantenerlo según tu Palabra.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Con todo mi corazón te he buscado. No permitas que me desvíe de tus Mandamientos.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 Tu Palabra atesoré en mi corazón Para no pecar contra Ti.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Bendito seas Tú, oh Yavé. Enséñame tus Estatutos.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 Con mis labios conté Todas las Ordenanzas de tu boca.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 Me he regocijado en el camino de tus Testimonios, Tanto como en todas [las] riquezas.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 Meditaré en tus Ordenanzas. Consideraré tus caminos.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 Me deleitaré en tus Estatutos. No olvidaré tu Palabra.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 Concede beneficio a tu esclavo, Que yo viva y guarde tu Palabra.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Abre mis ojos, Para que yo vea las maravillas de tu Ley.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 Soy un peregrino en la tierra. No encubras de mí tus Mandamientos.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 Mi alma se quebranta con el anhelo De seguir tus Ordenanzas en todo tiempo.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Tú reprendes a los arrogantes. Son malditos los que se desvían de tus Mandamientos.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Aparta de mí el oprobio y el menosprecio, Porque he guardado tus Testimonios.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Aunque los magistrados se sienten Y hablen contra mí, Tu esclavo medita en tus Estatutos.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Tus Testimonios son también mi deleite y mis consejeros.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 Postrada en el polvo está mi alma. Dame vida según tu Palabra.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 Te declaré mis caminos, Y me respondiste. Enséñame tus Estatutos.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Hazme entender la vía de tus Estatutos Para que yo medite en sus maravillas.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 Mi vida se disuelve a causa de la tristeza. Fortaléceme según tu Palabra.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Aparta de mí el camino falso, Y con bondad concédeme tu Ley.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 Escogí el camino fiel. Me enfrenté a tus Ordenanzas.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 Me apegué a tus Testimonios, oh Yavé. No me entregues a la vergüenza.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 Correré por el camino de tus Mandamientos, Porque Tú ensancharás mi corazón.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 Enséñame, oh Yavé, la vía de tus Estatutos, Y lo guardaré hasta el fin.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Dame entendimiento para que yo observe tu Ley, Y la observaré de todo corazón.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Hazme andar por la senda de sus Mandamientos, Porque en ella me deleito.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Inclina mi corazón a tus Testimonios, Y no a ganancia deshonesta.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Aparta mis ojos para que no miren vanidad. Revíveme en tus caminos.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Establece tu Palabra para tu esclavo, Como la que produce reverencia a Ti.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Aleja de mí la reprobación que temo, Porque tus Ordenanzas son buenas.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 Mira, yo anhelo tus Preceptos. Revíveme en tu justicia.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 Venga a mí, oh Yavé, tu misericordia, Tu salvación, conforme a tu Palabra,
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 A fin de que tenga respuesta para el que me reprueba, Porque confío en tu Palabra.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 No quites de mi boca en algún momento la Palabra de verdad, Porque yo confío en tus Ordenanzas.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 Así observaré tu Ley continuamente, Eternamente y para siempre.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 Andaré en libertad, Porque busco tus Preceptos.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 Delante de reyes hablaré también de tus Testimonios, Y no me avergonzaré.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 Me deleitaré en tus Mandamientos, Los cuales amo.
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 Alzaré mis manos hacia tus Mandamientos, Los cuales amo, Y meditaré en tus Estatutos.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 Recuerda la promesa [dada] a tu esclavo, En la cual me ordenaste esperar.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 Ella es mi consuelo en mi aflicción, Porque tu Palabra me da vida.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 Muchos se burlan de mí, Pero no me apartan de tu Ley.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 Recuerdo tus antiguas Ordenanzas, oh Yavé, Y me consuelo.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 Indignación ardiente se apoderó de mí A causa de los perversos que abandonan tu Ley.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Tus Estatutos fueron cantos para mí En la casa de mi peregrinaje.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 Recuerdo tu Nombre en la noche, oh Yavé, Y observo tu Ley.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 Esto me sucedió Para que yo observe tus Preceptos.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 Mi posesión es Yavé. Prometí que observaré tus Palabras.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 Busqué tu favor con todo mi corazón. Sé bondadoso conmigo, según tu Palabra.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 Consideré mis caminos Y volví mis pies a tus Testimonios.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 Me apresuré, no me demoré En guardar tus Mandamientos.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 Las cuerdas de los perversos me rodearon, Pero no olvidé tu Ley.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 A medianoche me levanto Para darte gracias por tus justas Ordenanzas.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Soy compañero de todos los que te temen, Y de los que observan sus Preceptos.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 Oh Yavé, la tierra está llena de tu misericordia. Enséñame tus Estatutos.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 Oh Yavé, bien hiciste a tu esclavo según tu Palabra.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Enséñame buen discernimiento y conocimiento, Porque creo tus Mandamientos.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Antes de ser afligido me extravié, Pero ahora observo tu Palabra.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Bueno eres Tú Y haces lo bueno. Enséñame tus Estatutos.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 Los arrogantes forjaron mentira contra mí. Yo observo tus Preceptos de todo corazón.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Los corazones de ellos están cubiertos de grasa. Yo me deleito en tu Ley.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 Fue bueno para mí que fui afligido, Para que aprenda tus Estatutos.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 Mejor me es la Ley de tu boca Que millares de oro y plata.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 Tus manos me hicieron y me afirmaron. Dame entendimiento para que aprenda tus Mandamientos.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 Que los que te reverencian Me vean y se alegren, Porque confié en tu Palabra.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 Sé, oh Yavé, que tus juicios con justos, Y que me afligiste según tu fidelidad.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Oh, que tu misericordia me consuele, Conforme prometiste a tu esclavo.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Que tu compasión venga a mí, Para que yo viva, Porque tu Ley es mi deleite.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Sean avergonzados los arrogantes, Porque sin causa me calumnian, Pero yo meditaré en tus Preceptos.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Que se vuelvan a mí los que te temen, Los que conocen tus Testimonios.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Sea mi corazón íntegro en tus Estatutos, Para que no sea avergonzado.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 Mi alma desfallece por tu salvación. Pero confío en tu Palabra.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Se consumen mis ojos [esperando] tu Palabra, Mientras digo: ¿Cuándo me consolará?
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Aunque soy como odre en el humo, No olvido tus Estatutos.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 ¿Cuántos son los días de tu esclavo? ¿Cuándo juzgarás a los que me persiguen?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Los arrogantes me cavaron fosa, Los que no concuerdan con tu Ley.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 Todos tus Mandamientos son fieles. Me persiguen con engaño. Ayúdame.
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 Casi me destruyen en la tierra, Pero yo no abandono tus Preceptos.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Vivifícame según tu misericordia, Y observaré los Testimonios de tu boca.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 Para siempre, oh Yavé, Tu Palabra permanece en el cielo.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 Por todas las generaciones es tu fidelidad. Tú estableciste la tierra, y permanece.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 Por tu mandato subsisten hasta hoy [todas las cosas], Porque todas ellas te sirven como esclavas.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Si tu Ley no fuera mi deleite, Entonces habría perecido en mi aflicción.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Jamás olvido tus Preceptos, Porque con ellos me vivificaste.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Tuyo soy. ¡Sálvame! Porque busqué tus Preceptos.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Me esperan los perversos para destruirme. Pero yo considero tus Testimonios.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 En toda perfección he visto límite. Tu Mandamiento es inmensamente amplio.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 ¡Oh, cuánto amo yo tu Ley! Todo el día es mi meditación.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Tus Mandamientos me hacen más sabio que mis enemigos, Porque siempre están conmigo.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 Tengo mejor entendimiento que todos mis maestros, Porque tus Testimonios son mi meditación.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 Entiendo más que los ancianos, Porque observo tus Preceptos.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 De todo mal camino contuve mis pies, Para observar tu Palabra.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 No me aparté de tus Ordenanzas, Porque Tú mismo me enseñaste.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 ¡Cuán dulces son tus Palabras a mi paladar, Más que miel a mi boca!
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 De sus Preceptos recibo entendimiento, Por tanto aborrezco todo camino falso.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 Lámpara a mis pies es tu Palabra, Y lumbrera a mi camino.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 Juré observar tus justas Ordenanzas. Lo cumpliré Y lo confirmo: Guardaré tus justas Ordenanzas.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 Estoy afligido en gran manera. Oh Yavé, vivifícame según tu Palabra.
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Acepta las ofrendas voluntarias de mi boca, oh Yavé, Y enséñame tus Ordenanzas.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 Mi vida está de continuo en peligro, Pero yo no olvido tu Ley.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Los perversos me tienden una trampa, Pero yo no me desvío de tus Preceptos.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 Tus Testimonios son mi herencia eterna, Porque ellos son el gozo de mi corazón.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 Incliné mi corazón a cumplir tus Estatutos, De continuo hasta el fin.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 Aborrezco a los de doble ánimo, Pero amo tu Ley.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 Tú eres mi Refugio y mi Escudo. Confío en tu Palabra.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Apártense de mí, perversos, Para que yo observe los Mandamientos de mi ʼElohim.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Susténtame según tu Palabra para que viva Y no dejes que sea avergonzado de mi esperanza.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Susténtame para que sea salvo, Para que yo observe de continuo tus Estatutos.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Rechazas a todos los que se desvían de tus Estatutos, Porque su astucia es falsedad.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Removiste de la tierra [como] escoria a todos los perversos. Por tanto, amo tus Testimonios.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 Mi carne se estremece de temor a Ti, Y ante tus juicios me lleno de pavor.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 Actué con justicia y rectitud. No me abandones a mis opresores.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Sé garante de tu esclavo para bien, Que no me opriman los arrogantes.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Mis ojos desfallecen por tu salvación, Y por la Palabra de tu justicia.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Haz con tu esclavo según tu misericordia, Y enséñame tus Estatutos.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Yo soy tu esclavo. Dame entendimiento para comprender tus Testimonios.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 Es tiempo de actuar, oh Yavé. Porque invalidaron tu Ley.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 Por tanto amo tus Mandamientos Más que el oro, sí, más que el oro fino.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 Por tanto estimo rectos todos tus Preceptos Con respecto a todas las cosas. Aborrezco todo camino falso.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 ¡Maravillosos son tus Testimonios! Por tanto los observa mi alma.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 La exposición de tus Palabras alumbra. Da entendimiento a los simples.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 Abrí bien mi boca y suspiré, Porque anhelaba tus Mandamientos.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Mírame y ten misericordia de mí, Como acostumbras con los que aman tu Nombre.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Afirma mis pasos con tu Palabra, Y no permitas que alguna iniquidad me domine.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Líbrame de la violencia de los hombres, Y observaré tus Mandamientos.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Haz resplandecer tu rostro sobre tu esclavo, Y enséñame tus Estatutos.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Manantiales de agua bajarán de mis ojos, Porque ellos no observan tu Ley.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 Justo eres Tú, oh Yavé, Y rectos son tus juicios.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Tus Testimonios nos mandaste con justicia, Y extraordinaria fidelidad.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Mi celo me consume, Porque mis adversarios olvidaron tus Palabras.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Tu Palabra es muy pura, Por tanto, tu esclavo la ama.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Soy pequeño y despreciado, [Pero] no olvido tus Preceptos.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Tu justicia es eterna, Y tu Ley es verdad.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 La aflicción y la angustia me alcanzaron, [Pero] tus Mandamientos son mi delicia.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 Tus Testimonios son justicia eterna. Dame entendimiento para que viva.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 Clamo con todo mi corazón. Respóndeme, oh Yavé. Observaré tus Estatutos.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 A Ti clamo: ¡Sálvame! Y observaré tus Testimonios.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 Me levanté antes del alba y clamé. Espero tu Palabra.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 Mis ojos se anticipan a las vigilias de la noche Para meditar en tu Palabra.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Oye mi voz según tu misericordia. Vivifícame, oh Yavé, según tus Ordenanzas.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 Los que siguen la perversidad se acercan. Están lejos de tu Ley.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 Tú, oh Yavé, estás cerca, Y todos tus Mandamientos son verdad.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 Desde antaño conocí tus Testimonios, Que Tú estableciste para siempre.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 Mira mi aflicción y rescátame, Porque yo no olvido tu Ley.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Defiende mi causa y redímeme, Vivifícame según tu Palabra.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 Lejos de los perversos está la salvación, Porque no buscan tus Estatutos.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Oh Yavé, grandes son tus misericordias. Vivifícame según tus Ordenanzas.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Muchos son mis perseguidores y mis adversarios, [Pero] yo no me aparto de tus Testimonios.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 Veo a los traidores y me disgusto, Porque ellos no observan tu Palabra.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Considera cuánto amo tus Preceptos. Vivifícame, oh Yavé, según tu misericordia.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 La suma de tu Palabra es verdad, Y eterna cada una de tus justas Ordenanzas.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 Príncipes me persiguen sin causa, Pero mi corazón tiene temor a tus Palabras.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 Me regocijo en tu Palabra Como el que halla gran despojo.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 Aborrezco y repugno la mentira. Amo tu Ley.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Siete veces al día te alabo A causa de tus justas Ordenanzas.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Mucha paz tienen los que aman su Ley, Y no hay tropiezo para ellos.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 Oh Yavé, espero tu salvación Y practico tus Mandamientos.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 Mi alma observa tus Testimonios, Y los ama intensamente.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 Observo tus Preceptos y tus Testimonios, Porque todos mis caminos están delante de Ti.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 Llegue mi clamor ante Ti, oh Yavé. Dame entendimiento según tu Palabra.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Llegue mi súplica ante Ti. Líbrame según tu Palabra.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Mis labios rebozan alabanza Cuando Tú me enseñas tus Estatutos.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 Hablará mi lengua tu Palabra, Porque todos tus Mandamientos son justicia.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Esté tu mano lista para socorrerme, Porque escogí tus Ordenanzas.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 Anhelo tu salvación, oh Yavé, Y tu Ley es mi deleite.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Viva mi alma y te alabe, Y que me ayuden tus Ordenanzas.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 Anduve errante como oveja perdida. Busca a tu esclavo, Porque no olvido tus Mandamientos.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.