< Salmos 118 >

1 Den gracias a Yavé, porque Él es bueno, Porque para siempre es su misericordia.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Diga ahora Israel: Que para siempre es su misericordia.
Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
3 Diga la casa de Aarón: Que para siempre es su misericordia.
Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
4 Digan ahora los que temen a Yavé: Que para siempre es su misericordia.
Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
5 En mi angustia clamé a YA, Y YA me respondió Y me colocó en lugar amplio.
Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
6 Yavé está conmigo, No temeré Lo que me haga el hombre.
Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
7 Yavé está conmigo entre los que me ayudan. Por tanto veré mi deseo en los que me odian.
Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
8 Mejor es refugiarse en Yavé Que confiar en hombre.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
9 Mejor es refugiarse en Yavé Que confiar en los poderosos.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
10 Todas las naciones me rodearon. En el Nombre de Yavé yo las destruiré.
Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
11 Me rodearon, Sí, me asediaron. En el Nombre de Yavé ciertamente las destruiré.
Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
12 Me rodearon como abejas. Se extinguieron como fuego de espinos. En el Nombre de Yavé yo ciertamente las destruiré.
Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
13 Ustedes me empujaron con violencia De modo que estaba cayendo, Pero me ayudó Yavé.
An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
14 Mi Fortaleza y mi Canto es YA. Él es mi salvación.
Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
15 Voz de júbilo y de salvación hay en las tiendas de los justos. La mano derecha de Yavé hace proezas.
Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
16 La mano derecha de Yavé está levantada en alto. La mano derecha de Yavé realiza hazañas.
An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
17 No moriré, sino viviré, Y contaré las obras de YA.
Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
18 Me disciplinó severamente YA, Pero no me entregó a la muerte.
Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
19 Ábranme las puertas de la justicia. Entraré por ellas, Daré gracias a YA.
Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
20 Esta es la puerta de Yavé. Por ella entrarán los justos.
Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
21 Te alabaré porque me escuchaste, Y fuiste mi salvación.
Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
22 La piedra que desecharon los edificadores Es cabeza del ángulo.
Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
23 Esta es la obra de Yavé. Es maravillosa ante nuestros ojos.
Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
24 Este es el día que hizo Yavé. ¡Regocijémonos y alegrémonos en él!
Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
25 Te imploramos, oh Yavé. ¡Sálvanos ahora! Te rogamos, oh Yavé que nos prosperes ahora.
Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
26 ¡Bendito el que viene en el Nombre de Yavé! Desde la Casa de Yavé los bendecimos.
Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
27 ʼEL es Yavé, y nos dio luz, Aten con cuerdas sacrificios festivos a los cuernos del altar.
Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
28 Tú eres mi ʼEL, y te doy gracias. Tú eres mi ʼElohim, te exaltaré.
Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
29 Den gracias a Yavé porque Él es bueno, Porque para siempre es su misericordia.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.

< Salmos 118 >