< Salmos 102 >

1 Escucha mi oración, oh Yavé, Y llegue mi clamor a Ti.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 No escondas de mí tu rostro en el día de mi angustia. Inclina a mí tu oído. El día cuando te invoco apresúrate a responderme.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Porque mis días se disuelven como humo, Y mis huesos arden como una chimenea.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Mi corazón está herido. Se marchita como la hierba. En verdad olvido comer mi pan.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Por la voz de mi gemido Mis huesos se pegaron a mi carne.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Soy semejante a la lechuza del desierto. Soy como un búho de las soledades.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 Estoy desvelado. Me siento como pájaro solo en un tejado.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Mis enemigos me afrentan todo el día. Los que contra mí se enfurecen Se conjuraron contra mí.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 He comido cenizas como pan Y mezclado mi bebida con lágrimas
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 A causa de tu indignación y de tu ira, Porque me levantaste y me lanzaste.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Mis días son una sombra que se prolonga, Y me marchito como hierba.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 Pero Tú, oh Yavé, permaneces para siempre, Y tu Nombre por todas las generaciones.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Te levantarás, tendrás misericordia de Sion, Porque es tiempo de tener compasión de ella, Pues llegó el tiempo señalado.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Ciertamente tus esclavos hallan deleite en sus piedras, Y tienen compasión del polvo de ella.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Así las naciones temerán al Nombre de Yavé, Y todos los reyes de la tierra [temerán] tu gloria.
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 Porque Yavé habrá edificado a Sion Será visto en su gloria.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 Ha considerado la oración de los desposeídos, Y no habrá despreciado su ruego.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Esto será escrito para la generación venidera, Para que un pueblo que está aún por nacer alabe a YA,
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 Porque miró desde lo alto de su Santuario. Desde el cielo Yavé miró a la tierra
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 Para escuchar el gemido de los presos, Para libertar a los sentenciados a muerte.
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 Que digan en Sion la fama de Yavé Y su alabanza en Jerusalén,
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 Cuando los pueblos y reinos sean juntamente congregados, Para servir a Yavé.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 Él debilitó mi fuerza en el camino. Acortó mis días.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Digo: Oh ʼEL mío, no me levantes en la mitad de mis días. Tus años son por todas las generaciones.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Desde la antigüedad fundaste la tierra, Y los cielos son obra de sus manos.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Ellos perecerán, Pero Tú permaneces. Todos ellos se desgastarán como una ropa, Como una ropa los cambiarás, Y pasarán.
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 Pero Tú eres el mismo, Y tus años no tendrán fin.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Los hijos de tus esclavos vivirán seguros, Y sus descendientes serán establecidos delante de Ti.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< Salmos 102 >