< Proverbios 22 >

1 Más vale el buen nombre que las muchas riquezas, Y el ser apreciado más que la plata y el oro.
An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
2 El rico y el pobre tienen esto en común: Yavé los hizo a todos ellos.
Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
3 El prudente ve el mal y se aparta, Pero los ingenuos siguen y reciben el daño.
Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
4 En las huellas de la humildad y del temor a Yavé, Andan riqueza, honor y vida.
Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
5 Espinos y lazos hay en el camino de los perversos, El que guarda su alma se aparta de ellos.
A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
6 Instruye al niño en el camino que debe seguir, Aun cuando sea viejo no se apartará de él.
Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
7 El rico domina al pobre, Y el que pide prestado es esclavo del prestamista.
Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
8 El que siembra maldad cosecha desgracia, Y la vara de su arrogancia se consumirá.
Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
9 El que tiene ojo generoso será bendecido, Porque repartió su pan con el pobre.
Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
10 Echa fuera al escarnecedor, y se irá la discordia, Y también saldrán la contienda y las afrentas.
Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
11 El que ama la pureza de corazón, El que tiene gracia en sus labios Tendrá como amigo al propio rey.
Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
12 Los ojos de Yavé velan por la verdad, Y Él descubre el engaño de los traicioneros.
Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
13 Dice el perezoso: Afuera hay un león. En plena calle me matará.
Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
14 Abismo profundo es la boca de la mujer ajena. El aborrecido de Yavé caerá allí.
Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
15 La necedad se pega al corazón del niño. La vara de la corrección se la apartará.
Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
16 El que oprime al pobre enriquece. Quien da al rico se empobrece.
Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
17 Inclina tu oído, escucha las palabras de los sabios Y aplica tu corazón a mis enseñanzas,
Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
18 Porque será bueno que las guardes dentro de ti, Y las establezcas sobre tus labios,
gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
19 Para que pongas en Yavé tu confianza. Te instruiré también a ti.
Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
20 ¿No te escribí cosas excelentes de consejos y enseñanzas,
Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
21 Para que conozcas la certeza de los dichos de verdad, Y las hagas llegar a los que te son enviados?
ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
22 No explotes al pobre, porque es pobre, Ni atropelles al desgraciado en la puerta,
Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
23 Porque Yavé defenderá su causa Y quitará la vida a los que la quitan a otro.
gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
24 No hagas amistad con el hombre iracundo, Ni te hagas acompañar del hombre violento,
Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
25 No sea que te acostumbres a sus caminos, Y coloques lazo a tu propia alma.
in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
26 No seas tú de los que dan la mano, Y salen fiadores de deudas.
Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
27 Si no tienes con qué pagar, ¿Por qué te quitarán tu propia cama?
gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
28 No remuevas el lindero antiguo Que colocaron tus antepasados.
Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
29 ¿Has visto hombre diligente en su obra? Estará delante de los reyes y no de la gentuza.
Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.

< Proverbios 22 >