< San Mateo 14 >
1 En aquel tiempo Herodes el tetrarca oyó la fama de Jesús
A lokacin nan ne, Hiridus mai mulki ya ji labarin Yesu.
2 y dijo a sus esclavos: Éste es Juan el Bautista, quien resucitó de entre [los] muertos, y por eso actúan en él esos poderes milagrosos.
Ya ce wa barorinsa, “Wannan Yahaya mai baftisma ne; ya tashi daga matattu. Saboda haka wadannan ikoki na aiki a cikinsa”.
3 Porque Herodes había arrestado a Juan y lo metió en prisión a causa de Herodías, la esposa de su hermano Felipe,
Domin Hiridus ya kama Yahaya, ya daure shi, kuma ya jefa shi a kurkuku saboda Hirudiya, matar dan'uwansa Filibus.
4 porque Juan le decía: No te es lícito vivir con ella.
Ya ce masa, “Bai kamata ka dauke ta a matsayin matarka ba.”
5 Quería matarlo, [pero] tenía temor al pueblo porque consideraban que él era profeta.
Da Hirudus ya kashe shi, amma yana tsoron jama'a, domin sun dauke shi a matsayin annabi.
6 Pero cuando llegó un cumpleaños de Herodes, la hija de Herodías danzó en el medio y agradó a Herodes,
Amma da ranar bikin haihuwar Hirudus ta kewayo, diyar Hirudiya tayi rawa a lokacin har ta burge Hirudus.
7 por lo cual le prometió con juramento que le daría lo que pidiera.
Sai ya yi mata alkawari har da rantsuwa cewa ta roki komenene ta ke so, zai ba ta.
8 Ella, instigada por su madre, dijo: ¡Dame ahora mismo la cabeza de Juan el Bautista en una bandeja!
Bayan ta amshi umurni daga wurin mahaifiyarta, ta ce, “Ka bani kan Yahaya mai baptisma a kan tire.
9 El rey se entristeció, pero a causa de los juramentos y de los reclinados, ordenó que se [le] diera.
Sarki ya husata da rokonta, amma domin rantsuwar da ya yi kuma domin mutanen da ke a wurin bukin tare da shi, sai ya umurta a yi haka.
10 Envió al [verdugo] quien decapitó a Juan en la cárcel.
Ya aika aka yanke kan Yahaya acikin kurkuku.
11 Su cabeza fue llevada en una bandeja. Fue entregada a la muchacha, y [ésta] la llevó a su madre.
Sai aka kawo kansa bisa tire, aka mika wa yarinyar, ta kuwa kai wa mahaifiyarta.
12 Sus discípulos llegaron, recogieron y sepultaron el cadáver, y le informaron a Jesús.
Sai almajiransa suka zo, su ka dauki gawar su ka je su ka yi jana'iza. Bayan haka, su ka je su ka fada wa Yesu.
13 Cuando Jesús oyó [esto], se retiró de allí en privado a un lugar solitario en una barca. La multitud lo [supo] y lo siguieron a pie desde las ciudades.
Sa'adda da Yesu ya ji haka, ya fita daga cikin kwale-kwale zuwa wani kebabben wuri. Da taron suka ji haka, suka bi shi da kafa daga biranen.
14 Desembarcó y vio una gran multitud. Se enterneció por ellos y sanó a sus enfermos.
Sai Yesu ya zo gabansu, ya kuma ga babban taron. Ya tausaya masu ya kuwa warkar da marasa lafiya dake cikinsu.
15 Al atardecer los discípulos se acercaron a Él y le dijeron: El lugar es solitario y la hora avanzada. Por tanto despide a la multitud para que vayan a las aldeas y compren su comida.
Da maraice ya yi, almajiransa su ka zo su ka ce masa, “Wannan wuri jeji ne, dare kuwa ya riga ya yi. Ka sallami taron domin su je cikin kauyukan nan, su sayo wa kansu abinci.”
16 Jesús les dijo: No tienen necesidad de ir. Denles ustedes de comer.
Amma Yesu ya ce masu, “Babu amfanin tafiyar su, ku basu abin da za su ci.”
17 Ellos le respondieron: No tenemos aquí sino cinco panes y dos peces.
Suka ce masa, “Muna da gurasa guda biyar da kifi biyu ne kawai.”
18 Entonces Él ordenó: Tráiganmelos acá.
Yesu ya ce, “Ku kawo mani su.”
19 Mandó que la multitud se recostara sobre la hierba. Tomó los cinco panes y los dos peces, levantó los ojos al cielo y los bendijo. Los partió y los dio a los discípulos, y los discípulos a la multitud.
Sai Yesu ya umarci taron su zauna akan ciyawa. Ya dauki gurasa biyar da kifi biyun. Ya dubi sama, ya sa albarka ya gutsuttsura ya kuma ba almajiran. Almajiran suka ba taron.
20 Comieron todos y se saciaron. Recogieron lo que sobró: 12 cestos llenos.
Dukansu suka ci suka koshi. Sai suka dauki gutsattsarin gurasa da kifin, kwanduna goma sha biyu cike.
21 Eran como 5.000 varones, sin contar las mujeres y los niños.
Wadanda su ka ci kuwa kimanin maza dubu biyar ne, ban da mata da yara.
22 De inmediato impulsó a los discípulos a subir a la barca, e ir delante de Él a la orilla opuesta mientras despedía a la multitud.
Nan take sai ya sa almajiran suka shiga kwale-kwalen su haye zuwa dayan gefen kafin shi, domin ya sallami taron.
23 Después que despidió a la multitud, subió a la montaña a hablar con Dios en privado. Cuando llegó la noche estaba allí.
Bayan ya sallami taron sun tafi, sai ya haura kan dutse domin yayi addu'a. Da dare yayi, yana can shi kadai.
24 Pero la barca, que estaba a varios kilómetros de la tierra, era zarandeada por las olas, porque el viento era contrario.
Amma yanzu fa kwale-kwalen na tsakiyar tekun, kuma da wuyar sarrafawa saboda rakuman ruwa da iska na gaba da su.
25 En la cuarta vigilia de la noche [Jesús] fue hacia ellos y andaba sobre el mar.
Da asuba (wajen karfe uku na dare) Yesu ya nufo su yana tafiya akan teku.
26 Cuando los discípulos vieron que Él andaba sobre el mar, se aterrorizaron y gritaron de miedo: ¡Es un fantasma!
Da almajiran suka ganshi yana tafiya akan tekun, sai suka firgita suna cewa, “Fatalwa ce,” suka yi kururuwa cikin tsoro.
27 Pero enseguida les habló: ¡Tengan ánimo, Yo soy, no teman!
Amma Yesu yayi magana da su nan da nan yace, “Ku yi karfin hali! Ni ne! Kada ku ji tsoro.”
28 Entonces Pedro le respondió: Señor, si eres Tú, manda que yo vaya a Ti sobre las aguas.
Bitrus ya amsa masa cewa, “Ubangiji, idan kai ne, ka umarce ni in zo wurin ka bisa ruwan.”
29 Él le dijo: ¡Ven! Pedro bajó de la barca, caminó sobre las aguas y fue a Jesús.
Yesu yace, “Zo” Sai Bitrus ya fita daga jirgin yana tafiya akan ruwan zuwa wurin Yesu.
30 Pero al ver el viento, se atemorizó. Cuando comenzó a hundirse, gritó: ¡Señor, sálvame!
Amma da Bitrus ya ga iska, sai ya tsorata. Yayin da ya fara nutsewa, sai ya tada murya ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
31 Al instante, Jesús extendió la mano. Lo tomó y le dijo: ¡Carente de fe! ¿Por qué dudaste?
Nan take Yesu ya mika hannunsa, ya kama Bitrus ya ce masa, “Kai mai karancin bangaskiya, meyasa ka yi shakka?”
32 Cuando ellos subieron a la barca cesó el viento.
Bayan da Yesu da Bitrus suka shiga cikin kwale-kwalen, sai iska ta daina kadawa.
33 Los que estaban en la barca lo adoraron y dijeron: Verdaderamente eres el Hijo de Dios.
Sai almajiran dake cikin kwale-kwalen su ka yi wa Yesu sujada suna cewa, “Hakika kai Dan Allah ne.”
34 Después de cruzar [el mar] llegaron a la tierra de Genesaret.
Da suka haye, sun iso kasar Janisarata.
35 Cuando los varones de aquel lugar lo reconocieron, notificaron a todo aquel territorio y le llevaron todos los enfermos.
Da mutanen wurin suka gane Yesu, sai suka aika da sako zuwa dukan yankin, kuma suka kawo masa dukan marasa lafiya.
36 Y le rogaban [que les permitiera ]aun tocar el borde de su ropa. Cuantos lo tocaron, fueron sanados.
Suka roke shi don su taba gezar rigarsa, kuma dukan wadanda suka taba shi sun warke.