< Marcos 14 >

1 Dos días después se celebraba la Pascua y los Panes sin Levadura. Los principales sacerdotes y los escribas buscaban cómo detenerlo por engaño y asesinarlo.
Idin Ketarewa da bukin gurasa mara yisti sauran kwana biyu kenan, sai shugabanin firistoci da malaman attaura suka nemi yadda zasu kama Yesu a asirce domin su kashe shi.
2 Decían: ¡No en la fiesta! No sea que se produzca un tumulto del pueblo.
Suna cewa amma “Ba a lokacin idin ba, domin kada su haddasa hargitsi a tsakanin mutane”.
3 Cuando Él estaba reclinado en Betania en la casa de Simón el leproso, se acercó una mujer con un frasco de alabastro con perfume de nardo puro muy costoso. Quebró el frasco de alabastro y [lo] derramó sobre su cabeza.
Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana shirin liyafa kenan sai ga wata mace dauke da kwalbar turare mai tamanin kwarai, ta shafa masa a kansa.
4 Algunos que se indignaron [decían]: ¿Para qué [ella] hizo este desperdicio de perfume?
wasu dake tare da Yesu suka husata, suna kwalbarta da cewa
5 Porque podría venderse por más de 300 denarios para dar a los pobres. La censuraban.
“Ai wannan turare ne mai tsada, ina laifin a sayar a raba wa talakawa kudin? ina dalilin wannan almubazaranci?
6 Pero Jesús dijo: Déjenla. No la molesten, porque buena obra hizo en Mí.
Sai Yesu yace masu “Ku kyaleta, don me kuke tsauta mata,
7 A los pobres siempre [los] tienen con ustedes, y cuando quieran pueden hacerles bien, pero a Mí no [me] tienen siempre.
ai Idan kuna da niyyar taimakon talakawa ko matalauta, suna nan tare da ku ko a yaushe amma ni bazan kasance da ku kullum ba.
8 Hizo lo que tenía disponible. Ungió mi cuerpo con anticipación para la sepultura.
Macen nan tayi aiki nagari domin shirya jikina ga jana'iza.
9 En verdad les digo: Dondequiera que se prediquen las Buenas Noticias se contará lo que hizo en memoria de ella.
hakika, Ina gaya maku, duk inda za'a yi bishara a duniya baza a mance da matan nan da hidimar da ta tayi mini ba.”
10 Entonces Judas Iscariote, uno de los 12, fue a los sumos sacerdotes para entregárselo.
Da jin haka sai Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin manzannin ya ruga zuwa wurin baban firist domin ya bashe shi a garesu,
11 Al oír [esto], ellos se regocijaron y prometieron darle plata. Y él buscaba una manera conveniente para entregarlo.
Da mayan firistoci suka ji haka suka yi murna matuka tare da alkawarin kudi ga Yahuza, shi kuwa sai ya fara neman zarafin da zai mika Yesu a gare su.
12 El primer día de los Panes sin Levadura, cuando celebraban la Pascua, los discípulos le preguntaron: ¿Dónde quieres que preparemos para comer la pascua?
A ranar farko ta bukin gurasa marar yisti da kuma hadayar ragon Idin ketarewa, almajiransa suka ce masa “Ina zamu shirya liyafar domin idin ketarewa?
13 Envió a dos de sus discípulos y les ordenó: Vayan a la ciudad, y un hombre que lleva un cántaro de agua los encontrará. Síganlo,
Ya aiki biyu daga cikin almajiransa da cewa “Ku shiga cikin birnin, zaku tarar da wani mutum dauke da tullun ruwa.
14 y donde entre, digan al señor de la casa que el Maestro dice: ¿Dónde está mi aposento para comer la pascua con mis discípulos?
Duk gidan da ya shiga ku bishi, sai ku cewa mai gidan, malam yace “ina bukatar masauki domin hidimar idin ketarewa tare da almajiraina?”'
15 Él les mostrará un gran aposento alto, amoblado y dispuesto. Preparen allí la pascua.
Zai kuwa nuna maku babban bene gyararre. Sai ku yi mana shiri a can.”
16 Los discípulos fueron a la ciudad. Encontraron como Él les dijo y prepararon la pascua.
Da shigar almajiran cikin birnin, sai kome ya kasance yadda ya fada, su kuwa suka yi shirye shiryen idin ketarewar.
17 Al llegar la noche, fue con los 12.
Da maraice ta yi, sai ya tare da sha biyun.
18 Cuando estaban reclinados y comían, Jesús dijo: En verdad les digo que uno de ustedes quien come conmigo, me entregará.
Yayin da suke zazzaune a teburin suna cin abincin, sai Yesu ya ce “Hakika ina gaya maku wani da ke ci tare da ni a nan zai bashe ni”.
19 Se entristecieron y le preguntaban: ¿Seré yo?
Sai suka damu suka tambaye shi daya bayan daya suna cewa “Hakika bani bane ko?”
20 Él les contestó: Es uno de los 12, quien moja el pan en el tazón conmigo.
Yesu ya amsa masu da cewa “Daya daga cikin sha biyu ne, wanda ke sa hannu tare da ni yanzu cikin tasar”.
21 En verdad, el Hijo del Hombre sigue [adelante], como está escrito de Él. Pero, ¡ay de aquél hombre quien entrega al Hijo del Hombre! Le sería mejor no haber nacido.
Dan Mutum zai tafi ne yadda nassi ya umarta game da shi amma kaiton wanda zai bashe shi! “zai, fiye masa, dama ba a haife shi ba”.
22 Mientras comían, Jesús tomó un pan, dio gracias, lo partió y dijo: Tomen, esto es mi cuerpo.
Lokacin da suke cin abincin, Yesu ya dauki gurasa ya sa albarka, ya gutsuttsura ta, sai ya basu yana cewa “Wannan jikinana ne”.
23 Después de tomar una copa y dar gracias, les dio, y todos bebieron de ella.
Ya kuma dauki koko, yayi godiya, ya basu, su kuwa suka sha daga kokon.
24 Y dijo: Esto es mi sangre del Pacto que es derramada por muchos.
Ya ce “Wannan jinina ne na alkawari da an zubar ga yawancin mutane”.
25 En verdad les digo: Que de ningún modo beba [Yo] más del fruto de la vid hasta aquel día cuando lo beba nuevo en el reino de Dios.
Hakika, bazan kara sha daga wannan ruwan inabi ba sai a ranar da zan sha sabo cikin mulkin Allah.”
26 Después de cantar un himno salieron hacia la Montaña de Los Olivos.
Bayan sun raira wakar yabo ga Allah, sai suka tafi wurin dutsen zaitun.
27 Jesús les dijo: Todos ustedes serán conturbados, porque está escrito: Heriré al Pastor, y las ovejas serán dispersadas.
Yesu ya ce masu dukkan ku zaku yi tuntube harma ku fadi saboda ni gama rubuce take cewa “Zan buge makiyayin, tumakin kuwa za su watse;
28 Pero después de ser resucitado, iré delante de ustedes a Galilea.
Amma bayan tashina, zai yi gaba in riga ku zuwa Galili.
29 Entonces Pedro le dijo: Si todos son conturbados, ciertamente yo no.
Bitrus ya ce masa “ko dukkansu sun fadi, faufau banda ni”.
30 Jesús le respondió: En verdad te digo que hoy, esta noche, antes que un gallo cante dos veces, me negarás tres veces.
Yesu yace masa “Hakika ina gaya maka, cikin wannan dare kafin carar zakara ta biyu zaka yi musun sani na sau uku”.
31 Pero Pedro insistía: Aunque sea necesario morir contigo, de ningún modo te negaré. Y lo mismo decían todos.
Amma Bitrus ya sake cewa “Koda za'a kasheni tare da kai ba zan yi musun sanin ka ba”. Dukkan su kuwa suka yi wannan Alkawari.
32 Entonces fueron a un sitio llamado Getsemaní, y [Jesús] dijo a sus discípulos: Siéntense aquí, hasta que Yo hable con Dios.
Suka isa wani wuri da ake kira Getsamani, sai Yesu ya ce wa almajiransa “Ku dakata anan domin zan je inyi addu'a”.
33 Tomó con Él a Pedro, Jacobo y Juan. Entonces [se] entristeció y [se ]angustió.
Sai ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya. Ya fara jin wahala mutuka tare da damuwa kwarai.
34 Les dijo: Mi alma está profundamente afligida hasta [la] muerte. Quédense aquí y velen.
Sai ya ce masu “Raina na shan wahala harma kamar in mutu. Ku dakata a nan, ku zauna a fadake”.
35 Después de ir un poco adelante, se postraba en tierra y hablaba con el Padre. [Pedía] que si fuera posible, pasara de Él aquella hora.
Da Yesu yayi gaba kadan, sai ya fadi kasa yayi addu'a yana cewa idan mai yiwuwa ne “A dauke masa wannan sa'a daga gare shi.
36 Y decía: ¡Abba! que significa Padre. ¡Todas las cosas son posibles para Ti! ¡Aparta de Mí esta copa! Pero no lo que Yo quiero, sino lo que Tú [quieras].
Ya ce “Ya Abba Uba, kome mai yuwane gare ka, ka dauke mini kokon wahalan nan, duk da haka ba nufina ba sai dai naka”.
37 [Jesús] volvió y los halló dormidos, y dijo a Pedro: Simón, ¿duermes? ¿No tuviste fuerzas para velar una hora?
Da komowarsa ya same su suna barci, sai ya ce wa Bitrus, Siman barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a fadake ko da sa'a daya ba?
38 Velen y hablen con Dios para que no entren en tentación. El espíritu a la verdad está dispuesto, pero la carne es débil.
Ku zauna a fadake, kuyi addu'a kada ku fada cikin jaraba. Lalle ruhu na da niyya amma jiki raunana ne.
39 Fue otra vez y dijo las mismas palabras.
Sai ya sake komawa, yayi addu'a, yana maimaita kalmominsa na farko.
40 Al regresar otra vez, los halló dormidos, porque sus ojos estaban pesados, y no sabían qué responderle.
Har wa yau kuma ya sake dawowa, ya same su suna barci don barci ya cika masu idanu kwarai, sun kuwa kasa ce masa kome.
41 Volvió la tercera vez y les dijo: Duerman y descansen lo que resta. ¡Es suficiente! Llegó la hora. Ya el Hijo del Hombre es entregado en las manos de los pecadores.
Ya sake komowa karo na uku yace masu “har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka! Lokaci yayi, an bada Dan Mutum ga masu zunubi”.
42 ¡Levántense! Vamos. Miren, el que me entrega se acerca.
Ku tashi mutafi kun ga, ga mai bashe ni nan ya kusato.”
43 Al instante, mientras aún Él hablaba, llegó Judas, uno de los 12, acompañado por una turba con espadas y garrotes enviados por los principales sacerdotes, los escribas y los ancianos.
Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, daya daga cikin sha biyun da taron jama'a rike da takkuba da kulake. Manyan firistoci da malaman attaura da shugabanni suka turo su.
44 El que lo entregaba les dio una señal: Es Aquel a Quien yo bese. Arréstenlo y llévenlo bajo guardia.
Mai bashe shi din nan ya riga ya kulla da su cewa “Wanda zan yi wa sumba shine mutumin, ku kama shi ku tafi da shi a tsare.
45 De inmediato, se acercó Judas y le dijo: ¡Maestro! Y lo besó aparatosamente.
Da isowarsa kuwa, sai ya zo wurin Yesu ya ce “Ya malam!”. Sai ya sumbace shi.
46 Entonces le pusieron las manos encima y lo arrestaron.
Su kuwa suka kama shi, suka tafi da shi.
47 Pero uno de los presentes sacó la espada, atacó al esclavo del sumo sacerdote y le amputó la oreja.
Amma daya daga cikin na tsaye ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya yanke masa kunne.
48 Jesús les preguntó: ¿Como contra un bandido salieron con espadas y garrotes a detenerme?
Sai Yesu ya ce “kun fito kamar masu kama yan fashi da takkuba da kulake, domin ku kama ni?
49 Cada día estaba con ustedes y enseñaba en el Santuario, y no me arrestaron. Pero [esto sucede] para que se cumplan las Escrituras.
Lokacin da nake koyarwa a Haikali, kowace rana da ku, baku kama ni ba. Amma anyi haka ne domin a cika abinda Nassi ya fada.”
50 Todos lo abandonaron y huyeron.
Daga nan duk wadanda suke tare da Yesu suka yashe shi, suka tsere.
51 Un joven lo seguía cubierto con una sábana. Y lo arrestaron,
Wani saurayi, daga shi sai mayafi ya bi shi, suka kai masa cafka.
52 pero él soltó la sábana y huyó desnudo.
Shi kuwa ya bar masu mayafin ya gudu tsirara.
53 Llevaron a Jesús ante el sumo sacerdote. [Allí] se reunieron todos los principales sacerdotes, los ancianos y los escribas.
Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. a can suka tara dattawa duk da manyan firistoci da shugabanni da marubuta, suka taru a wurinsa.
54 Pedro lo siguió de lejos, hasta el patio del sumo sacerdote, y se sentó con los guardias para calentarse junto al fuego.
Bitrus kuwa ya bi shi daga nesa har cikin gidan babban firist. Ya zauna tare da dogaran Haikalin, yana jin dumin wuta.
55 Los principales sacerdotes y el Tribunal Supremo buscaban testigos contra Jesús para asesinarlo, pero no [los] hallaban.
Sai, manyan firistoci da duk 'yan majalisa Yahudawa suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi. Amma basu samu ba.
56 Porque muchos daban falso testimonio contra Él, pero los testimonios no eran iguales.
Da yawa kuma suka yi masa shaidar Zur (Karya), amma bakin su bai zama daya ba.
57 Algunos que dieron falso testimonio contra Él dijeron:
Sai wadansu kuma suka taso suka yi masa shaidar zur (karya) suka ce.
58 Nosotros lo oímos cuando dijo: Yo destruiré este Templo hecho por manos humanas, y en tres días edificaré otro no hecho por manos.
“Mun ji ya ce, wai zai rushe haikalin nan da mutane suka gina, ya sake gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba”.
59 Pero aun así su testimonio no coincidía.
Duk da haka, sai shaidar tasu bata zo daya ba.
60 El sumo sacerdote se levantó y preguntó a Jesús: ¿Nada respondes a lo que testifican contra ti?
Sai babban firist ya mike a tsakanin su, ya tambayi Yesu yace “Ba ka da wata amsa game da shaidar da mutanen nan suke yi a kanka?
61 Pero Él guardó silencio y nada respondió. El sumo sacerdote le preguntaba otra vez: ¿Eres Tú el Cristo, el Hijo del Bendito?
Amma yayi shiru abinsa, bai ce kome ba. Sai babban firist din ya sake tambayarsa “To, ashe kai ne Allmasihu Dan Madaukaki?
62 Jesús respondió: Yo soy. Verán al Hijo del Hombre sentado a la mano derecha del Padre y que viene en las nubes del cielo.
Yesu ya ce “Nine. Za ku kuwa ga Dan Mutum zaune dama ga mai iko, yana kuma zuwa cikin gajimare”.
63 Entonces el sumo sacerdote rasgó sus ropas y dijo: ¿Qué necesidad tenemos de testigos?
Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa yace “Wacce shaida kuma zamu nema?
64 Ustedes oyeron la blasfemia. ¿Qué les parece? Y todos ellos lo declararon reo de muerte.
Kun dai ji sabon da yayi! Me kuka gani? Duk suka yanke masa hukunci akan ya cancanci kisa.
65 Algunos comenzaron a escupirlo, a cubrirle el rostro, a darle puñetazos y a decirle: ¡Profetiza! También los alguaciles lo recibieron a bofetadas.
Wadansu ma suka fara tottofa masa yau, suka daure masa idanu, suka bubbuge shi suna cewa “Yi annabci” Dogaran kuma suka yi ta marinsa.
66 Mientras Pedro estaba abajo en el patio, apareció una de las esclavas del sumo sacerdote.
Bitrus kuwa na kasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo.
67 Cuando vio que Pedro se calentaba, lo miró fijamente y le dijo: ¡Tú también estabas con Jesús de Nazaret!
Da ta ga Bitrus na jin dumi, ta yi masa kallon gaske ta ce “Kaima ai tare kake da banazaren nan Yesu”.
68 Pero él negó: No sé ni entiendo lo que dices. Y salió a la puerta.
Amma ya musa ya ce “Ni ban ma san abinda kike fada ba balle in fahimta”. Sai ya fito zaure. Sai zakara yayi cara.
69 Al verlo otra vez, la esclava repitió a los presentes: ¡Éste es [uno] de ellos!
Sai baranyar ta ganshi, ta sake ce wa wadanda ke tsaitsaye a wurin, “Wannan ma daya daga cikinsu ne”.
70 Pero él negó otra vez. Un poco después, los que estaban presentes dijeron otra vez a Pedro: ¡Verdaderamente eres de ellos, pues también eres galileo!
Amma ya sake musawa, jim kadan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus “Lalle kai ma dayansu ne don ba Galile ne kai”.
71 Y él juró con maldición: ¡No conozco a este Hombre de Quien ustedes hablan!
Sai ya fara la'anta kansa yana ta rantsuwa yana ce wa “Ban ma san mutumin nan da kuke fada ba”.
72 Enseguida el gallo cantó por segunda vez, y Pedro se acordó de lo que Jesús le dijo: Antes que el gallo cante dos veces, me negarás tres veces. Reflexionó y lloraba.
Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu, Bitrus kuwa ya tuna da maganar Yesu a gare shi cewa “Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sani na sau uku”. Da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.

< Marcos 14 >