< Marcos 13 >

1 Cuando Él salió del Templo uno de sus discípulos le dijo: Maestro, ¡mira cuán grandes piedras y cuán grandes edificios!
da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa “malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!”
2 Jesús le contestó: ¿Ves estos grandes edificios? Que de ningún modo quede aquí piedra sobre piedra que no sea derribada.
Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba.”
3 Cuando Él estaba sentado en la Montaña de Los Olivos, frente al Santuario, Pedro, Jacobo, Juan y Andrés le preguntaban en privado:
Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce.
4 Dinos, ¿cuándo sucederá esto? ¿Y cuál será la señal que indica que todas estas cosas se van a cumplir?
Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?''
5 Entonces Jesús les respondió: Cuidado que nadie los engañe.
Yesu ya ce masu, “ku kula, kada kowa ya rudeku.
6 Vendrán muchos en mi Nombre y dirán: Yo soy. Engañarán a muchos.
Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.
7 Cuando oigan de guerras y rumores de guerras, no se turben. Es necesario que sucedan, pero aún no es el fin.
In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba.
8 Porque se levantará nación contra nación, y reino contra reino. Habrá terremotos en diversas regiones. Habrá hambrunas. Estas cosas serán principio de dolores de parto.
Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.
9 Pero ustedes tengan cuidado. Los entregarán a los tribunales supremos, los azotarán en congregaciones y serán puestos en pie delante de gobernadores y reyes por causa de Mí, para testimonio a ellos.
Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su.
10 Primero tienen que proclamarse las Buenas Noticias a todas las naciones.
Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.
11 Cuando los conduzcan para entregarlos, no se preocupen por lo que deben hablar, sino hablen lo que les sea dado en aquella hora. Porque no son ustedes los que hablan, sino el Espíritu Santo.
Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne.
12 [El] hermano entregará a su hermano a [la] muerte, y [el] padre al hijo, y [los] hijos se rebelarán contra [sus] progenitores y los matarán.
Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su.
13 [Ustedes] serán aborrecidos por todos a causa de mi Nombre, pero el que persevere hasta [el] fin será salvo.
Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.
14 Pero cuando vean la [repugnancia] devastadora en pie donde no debe (el que lee, entienda), entonces los que estén en Judea huyan a las montañas.
Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse.
15 Quien esté en la azotea, no baje ni entre a recoger algo de su casa,
Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu.
16 y el que esté en el campo, no regrese a tomar su ropa.
Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.
17 Pero, ¡ay de las que estén embarazadas y de las que amamanten en aquellos días!
Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin.
18 Hablen con Dios para que no sea en invierno.
Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina.
19 Porque aquellos días serán una tribulación como no hubo desde [el] principio de [la] creación que Dios hizo, hasta ahora y que de ningún modo haya jamás.
A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada.
20 Si el Señor no acortara aquellos días, nadie sería salvo, pero por causa de los escogidos los acortó.
In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.
21 Entonces, si alguien les dice: ¡Mira, aquí está el Cristo! ¡Mira, está allí! No [lo] crean.
To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata.
22 Porque se levantarán falsos cristos y falsos profetas. Mostrarán señales y prodigios a fin de extraviar a los escogidos, si fuera posible.
Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki.
23 Pero ustedes estén alerta. Les predije todas las cosas.
Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.
24 Pero en aquellos días, después de aquella tribulación, el sol se oscurecerá, la luna no dará su claridad nocturna,
Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba.
25 las estrellas caerán del cielo, y las potencias que están en los cielos serán sacudidas.
Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.
26 En ese tiempo verán al Hijo del Hombre que viene en [las] nubes con gran poder y gloria.
Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka.
27 Entonces enviará a los ángeles y reunirá a los escogidos de los cuatro puntos cardinales, desde [el] extremo de [la] tierra hasta [el] extremo del cielo.
Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.
28 De la higuera aprendan la parábola: Cuando ya su rama enternece y brotan sus hojas, saben que el verano está cerca.
“Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan.
29 Así también ustedes, cuando vean que suceden estas cosas, sepan que está cerca, a [las] puertas.
Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.
30 En verdad les digo: Que de ningún modo pase este linaje hasta que se cumplan todas estas cosas.
Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
31 El cielo y la tierra pasarán, pero mis palabras de ningún modo pasarán.
Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
32 Con respecto a aquel día o la hora, nadie sabe, ni los ángeles en [el] cielo, ni el Hijo, sino el Padre.
Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.
33 Cuidado, estén alerta, porque no saben cuándo es el tiempo.
Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba.
34 Sucederá como cuando un hombre viaja y deja su casa. Da a sus esclavos la autoridad, a cada uno su trabajo y ordena al portero que vigile.
Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.
35 Velen, pues, porque no saben cuándo viene el señor de la casa: si en la tarde, a media noche, al canto del gallo o en la mañana,
To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne.
36 no sea que, al llegar de repente, los halle dormidos.
Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci.
37 Lo que digo a ustedes, digo a todos: ¡Velen!
Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!”

< Marcos 13 >