< Job 4 >

1 Entonces intervino Elifaz temanita:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Si intentamos razonar contigo te será molesto. Pero, ¿quién puede refrenarse de hablar?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Ciertamente tú enseñabas a muchos y fortalecías las manos débiles.
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 Tus palabras levantaban al que tropezaba y afirmabas las rodillas decaídas.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 Pero ahora te sucede a ti. Te desalientas, te tocó a ti y te turbas.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 ¿No es tu temor a ʼElohim tu confianza, y la integridad de tus procedimientos tu esperanza?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Te ruego que recuerdes: ¿Quién pereció jamás por ser inocente? ¿Dónde fueron destruidos los rectos?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 Según veo, los que aran iniquidad y siembran aflicción, las cosechan.
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 Por el aliento de ʼElohim perecen, y por el soplo de su ira son consumidos.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 El rugido del león, la voz fiera de la leona y los dientes de sus cachorros son quebrados.
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 El león viejo perece por falta de presa, y los cachorros de la leona se dispersan.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 Entonces un mensaje me llegó a hurtadillas, y mi oído percibió un susurro de él
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 en inquietantes visiones nocturnas, cuando el sueño profundo cae sobre los hombres.
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 Un terror se apoderó de mí, y todos mis huesos se estremecieron.
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 Al pasar un espíritu frente a mí se eriza el pelo de mi cuerpo.
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 Se detiene, pero no distingo su semblante. Una apariencia está delante de mis ojos, hay silencio… y oigo una voz reposada:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 ¿Será el hombre más justo que ʼElohim? ¿El hombre, más puro que su Hacedor?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 Ciertamente en sus esclavos no confía, y a sus ángeles atribuye insensatez.
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 ¡Cuánto más los que viven en casas de barro cimentadas en el polvo serán desmenuzados por la polilla!
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 Entre la mañana y la tarde son destruidos, y sin que alguno se dé cuenta, perecen para siempre.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 ¿No les son arrancadas las cuerdas de sus tiendas? En ellas mueren, pero no adquirieron sabiduría.
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’

< Job 4 >