< Job 13 >

1 Ciertamente mis ojos vieron todo esto. Mis oídos lo escucharon y entendieron.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 Como ustedes lo saben, yo también lo sé. En nada soy menos que ustedes.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Pero en verdad yo me dirijo a ʼEL-Shadday, porque quiero disputar con ʼElohim.
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 Ustedes son forjadores de mentiras. Médicos inútiles son todos ustedes.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 ¡Ojalá callaran por completo! Esto sería sabiduría.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Escuchen mi argumento y atiendan las contenciones de mis labios.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 ¿Dirán ustedes perversidades a favor de ʼElohim? ¿Hablarán engaño a favor de Él?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 ¿Mostrarán parcialidad a su favor? ¿Contenderán ustedes a favor de ʼElohim?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 ¿Les irá bien cuando Él los escudriñe? ¿Se burlarán de Él como el que se burla de un hombre?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 Ciertamente los reprenderá, si en secreto son parciales.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 ¿No los aterrorizará su majestad, y caerá su terror sobre ustedes?
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Sus dichos memorables serán proverbios de polvo, y sus defensas serán de barro.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Callen y hablaré yo. ¡Y que me venga lo que venga!
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 ¿Por qué debo tomar mi carne entre mis dientes, y colocar mi vida en mis manos?
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Ciertamente aunque me mate, en Él esperaré, pero defenderé mis caminos delante de Él.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 Esto también será mi salvación, porque no llegará ante su presencia el impío.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Escuchen con atención lo que digo. Mi declaración entre en sus oídos:
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Ciertamente preparé mi defensa. Sé que seré declarado justo.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 ¿Quiere alguno contender conmigo? Porque si ahora callo, moriría.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Solo dos cosas no hagas conmigo, y no me esconderé de tu Presencia:
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Aparta de sobre mí tu mano, y no me espante tu terror.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Llama luego y yo responderé, o yo hablaré y Tú me responderás.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 ¿Cuántas son mis iniquidades y pecados? Hazme saber mi transgresión y mi pecado.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 ¿Por qué ocultas tu rostro y me consideras tu enemigo?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 ¿Quebrantas una hoja volandera, y persigues un pasto seco?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 Escribes contra mí cosas amargas y me haces heredar las iniquidades de mi juventud.
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 Colocas mis pies en el cepo. Vigilas todos mis caminos. Trazas un límite para las plantas de mis pies.
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 Mi cuerpo se desgasta como cosa podrida, como ropa vieja comida de polilla.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.

< Job 13 >