< Job 12 >
2 Entonces ciertamente ustedes son el pueblo, y con ustedes se acaba la sabiduría.
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 Pero yo tengo entendimiento como ustedes. No soy menos que ustedes. ¿Quién no sabe tales cosas?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 Yo soy alguien que para su amigo es motivo de risa, uno que clamó a ʼElohim y le respondió. ¡El justo e intachable es un payaso!
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 El que tiene bienestar desprecia la calamidad como algo preparado para aquellos que resbalan.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 Prosperan las tiendas de los ladrones y los que provocan a ʼEL están seguros, aquellos que ʼEloah trae a su poder.
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 En efecto, pregunta ahora a las bestias, y ellas te enseñarán, a las aves del cielo, y ellas te lo dirán.
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 O habla a la tierra, y te enseñará. Los peces del mar también te lo declararán.
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 ¿Cuál de ellos no sabe que la mano de Yavé hizo esto,
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 que en su mano está la vida de todo viviente y el hálito de toda la humanidad?
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 ¿No distingue el oído las palabras y el paladar prueba la comida?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 En los ancianos está la sabiduría y en la larga edad el entendimiento.
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 Con Él están la sabiduría y el poder. Suyos son el consejo y el entendimiento.
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 Si Él derriba, no será reedificado. Si Él encierra al hombre, no hay liberación.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 Si Él retiene las aguas, se secan, y si las suelta, inundan la tierra.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 Con Él están la fortaleza y la sana sabiduría. Suyos son el que yerra y el que hace errar.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 Hace andar descalzos a los consejeros y entontece a los jueces.
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 Suelta las ataduras que imponen los reyes y ata con una cuerda sus cinturas.
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 Hace ir descalzos a los sacerdotes y derriba a los poderosos.
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 Priva del habla a los de confianza, y del discernimiento a los ancianos.
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 Derrama desprecio sobre los nobles y afloja el cinturón de los fuertes.
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 Descubre las profundidades de la oscuridad y saca a la luz la sombra de muerte.
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 Engrandece las naciones y las destruye. Ensancha los pueblos y los suprime.
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 Priva de discreción a los caudillos de los pueblos de la tierra y los hace deambular por un desierto sin camino.
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 No tienen luz. Palpan en la oscuridad, y los hace tambalearse como ebrios.
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.