< Hechos 8 >

1 Saulo estuvo de acuerdo con este asesinato. Aquel día se desató una gran persecución contra la Iglesia de Jerusalén. Todos se dispersaron por las regiones de Judea y Samaria, excepto los apóstoles.
Bulus ya amince da mutuwarsa. A wannan rana tsanani mai zafi ya fara tasowa akan Iklisiya da take a Urushalima, sai masu bangaskiya duka suka bazu ko ina a cikin garuruwan Yahudiya da Samariya, sai manzannin kadai aka bari.
2 Unos hombres piadosos sepultaron a Esteban e hicieron gran lamentación por él.
Amintattun mutane suka bizne Istifanus suka yi babban makoki game da shi.
3 Saulo asolaba a la iglesia. Entraba de casa en casa, arrastraba a hombres y mujeres y [los] entregaba en [la] cárcel.
Amma Shawulu ya yi wa Iklisiya mugunta kwarai, ya dinga shiga gida gida yana jawo mutane maza da mata, kuma yana kulle su cikin kurkuku.
4 Pero los esparcidos proclamaban la Palabra dondequiera que iban.
Duk da haka masu bangaskiyar nan da suka warwatsu suka tafi suka dinga yada wa'azin maganar.
5 Felipe bajó a una ciudad de Samaria y les predicaba a Cristo.
Filibus ya tafi can Samariya ya yi shelar Almasihu.
6 La multitud, cuando oyó y vio las señales milagrosas que hacía, prestaba atención unánime a lo expresado por Felipe.
Da taron mutane suka ji kuma suka ga alamun da Filibus yake yi, sai suka mai da hankali dukansu domin su ji abinda yake fadi.
7 Porque muchos espíritus impuros daban alaridos y salían de los poseídos. Muchos paralíticos y cojos eran sanados.
Domin kazaman ruhohi sun fito daga cikin mutane da yawa da suka saurare shi suna kuka da kururuwa; nakasassun mutane dayawa da guragu suka warke.
8 Hubo grande gozo en aquella ciudad.
Kuma aka yi farin ciki mai girma a birnin.
9 Pero un hombre llamado Simón practicaba la magia y asombraba a la gente de Samaria y se hacía pasar como un gran personaje.
Amma akwai wani mutum a cikin birnin da ake kira Siman, wanda tun farko shi masafi ne da kuma dan dabo, yana yi wa mutanen Samariya abubuwan ban mamaki, yayin da yake kiran kansa wani mai muhimmanci.
10 Todos, desde el más pequeño hasta el más grande, le ponían atención y decían: Éste es el gran poder de Dios.
Dukan Samariyawa, manya da yara, suna sauraronsa, su kan ce, ''Wannan mutum shine ikon Allahn nan wanda ake kira mai girma.''
11 Le prestaban mucha atención porque los asombró con las magias durante mucho tiempo.
Suna sauraron sa, domin ya dade yana yi masu abubuwan mamaki da tsafe-tsafensa.
12 Pero hombres y mujeres creyeron las Buenas Noticias del reino de Dios en el Nombre de Jesucristo que Felipe les proclamaba, y se bautizaban.
Amma da suka yi bangaskiya da wa'azin bisharar da Filibus yake yi game da mulkin Allah da sunan Yesu Almasihu, sai aka yi masu Baftisma dukansu maza da mata.
13 Aun el mismo Simón creyó, y después de ser bautizado, estaba adherido constantemente a Felipe. Se maravillaba al ver las señales milagrosas y los grandes prodigios que hacía.
Har shima Siman da kansa ya ba da gaskiya. Bayan an yi masa Baftisma ya cigaba da bin Filibus, da ya ga ana nuna alamu da manyan ayyuka, sai ya yi mamaki.
14 Cuando los apóstoles en Jerusalén supieron que Samaria había recibido la Palabra de Dios, les enviaron a Pedro y Juan.
Da manzannin da ke Urushalima suka ji labarin Samariya ta karbi maganar Allah, sai suka aika masu Bitrus da Yahaya.
15 Llegaron y hablaron con Dios por ellos para que recibieran [el] Espíritu Santo,
Da suka iso, suka yi masu addu'a, domin su karbi Ruhu Mai Tsarki.
16 porque aún no había descendido sobre ellos. Solo habían sido bautizados en el Nombre del Señor Jesús.
Domin har wannan lokaci, Ruhu Mai Tsarki bai sauko kan kowannensu ba; an dai yi masu baftisma ne kadai cikin sunan Ubangiji Yesu.
17 Luego les impusieron las manos y recibieron [el] Espíritu Santo.
Sai Bitrus da Yahaya suka dora masu hannuwansu, sai suka karbi Ruhu Mai Tsarki.
18 Entonces Simón, quien vio que por la imposición de las manos de los apóstoles era dado el Espíritu, les ofreció dinero
Sa'adda Siman yaga ana bayar da Ruhu Mai Tsarki ta wurin dorawar hannuwan manzanni, ya basu kudi.
19 y dijo: Denme también este poder para que a cualquiera a quien imponga las manos reciba el Espíritu Santo.
Ya ce, “Ku bani wannan iko, ni ma, don duk wanda na dora wa hannu ya karbi Ruhu Mai Tsarki.''
20 Entonces Pedro le contestó: Tu dinero permanezca contigo para destrucción, porque pensaste que el Don de Dios se compra por dinero.
Amma Bitrus yace masa, ''Azurfarka ta lalace tare da kai, saboda kana tunanin za ka malaki baiwar Ubangiji da kudi.
21 Tú no tienes parte ni participación en este asunto, porque tu corazón no es recto delante de Dios.
Baka da wani rabo a wannan al'amari, domin zuciyarka ba daidai take da Allah ba.
22 Por tanto cambia de mente en cuanto a esta maldad y ruega al Señor. Tal vez te sea perdonado lo que pensaste.
Saboda haka ka tuba daga wannan muguntarka, ka kuma yi addu'a ga Ubangiji, domin mai yiwuwa ya gafarta maka game da manufar zuciyarka.
23 Porque veo que estás en hiel de amargura y en atadura de maldad.
Domin na gane kana cikin bacin rai da kuma cikin daurin zunubi.''
24 Simón respondió: Rueguen ustedes al Señor por mí para que no me sucedan estas cosas.
Siman ya amsa ya ce, ''Kayi addu'a ga Ubangiji domina, kada wani daga cikin abubuwan nan da ka fada ya faru da ni.''
25 Después de testificar solemnemente y hablar la Palabra del Señor, regresaron a Jerusalén. En el camino proclamaron las Buenas Noticias en muchas aldeas de samaritanos.
Sa'anda Bitrus da Yahaya suka bada shaida kuma suka fadi maganar Ubangiji, sun koma Urushalima; akan hanya, suka yi wa'azin bishara a kauyukan samariyawa da yawa.
26 Un ángel del Señor habló a Felipe: Vé hacia el sur por el camino solitario que baja de Jerusalén a Gaza.
Yanzu kuwa Mala'ikan Ubangiji ya yi wa Filibus magana cewa, ''Tashi ka tafi ta kudu da hanyar da ta yi kasa daga Urushalima zuwa Gaza'' (wannan hanyar yana cikin hamada.)
27 Fue y vio a un eunuco etíope, funcionario tesorero de Candace, reina de los etíopes, quien había ido a adorar en Jerusalén.
Ya kuwa tashi ya tafi. Sai ga wani mutum daga Habasha, baba ne mai babban matsayi a karkashin Kandakatu, sarauniyar Habasha. Shine yake mulkin dukan dukiyarta. Ya zo Urushalima domin ya yi ibada.
28 Mientras regresaba en su carruaje leía el profeta Isaías.
Yana komawa zaune cikin karussarsa, kuma yana karanta Littafin annabi Ishaya.
29 Entonces el Espíritu dijo a Felipe: Vé y júntate a este carruaje.
Ruhun ya ce wa Filibus, ''Ka je kusa da karussar nan.''
30 Felipe corrió y oyó que leía el profeta Isaías. Le preguntó: ¿Entiendes lo que lees?
Sai Filibus ya gudu ya same shi, kuma ya ji shi yana karanta littafin annabi Ishaya, sai ya ce, ''Ka fahimci abin da kake karantawa?''
31 Y él contestó: ¿Cómo podría si alguno no me explica? Y rogó a Felipe que subiera a sentarse con él.
Bahabashen ya ce. ''Yaya zan iya, idan ba wani ya bishe ni ba?'' Ya roki Filibus ya shigo cikin karussar ya zauna tare da shi.
32 La porción de la Escritura que leía era ésta: Como oveja fue llevado al matadero, y como cordero silencioso ante el que lo trasquila no abrió su boca.
Wannan kuwa shine nassin da Bahabashen yake karantawa, ''An kai shi kamar tunkiya zuwa mayanka; shiru kuma, kamar dan rago a hannun masu sosayarsa, bai bude baki ba.
33 En la humillación no se le hizo justicia. ¿Quién describirá su generación? Porque su vida fue removida de la tierra.
Cikin kaskancinsa aka yi masa shari'a da rashin adalci: Wa zai bada tarihin tsararsa? Domin an dauke ransa daga duniya.''
34 El eunuco preguntó a Felipe: Te ruego, ¿De quién dice esto el profeta? ¿De él mismo o de otro?
Sai baban ya tambayi Filibus, ya ce, ''Na roke ka, gaya mani, game da wa annabin yake magana? Da kansa, ko kuwa wani mutum dabam?''
35 Entonces Felipe comenzó desde esta Escritura, y le anunció las Buenas Noticias de Jesús.
Filibus ya fara magana; akan littafin Ishaya, ya kuwa yi masa wa'azi akan Yesu.
36 Cuando iban por el camino, llegaron a un lugar donde había agua, y el eunuco dijo: ¡Aquí hay agua! ¿Qué impide que sea bautizado?
Yayin da suke tafiya akan hanya, sai suka iso bakin wani kogi; Baban ya ce, “Duba, ga ruwa anan; me zai hana ayi mani baftisma?”
Filibus ya ce,” Idan ka gaskanta da zuciya daya, ana iya yi maka baftisma.” Sai Bahabashen ya ce, “Na gaskata Yesu Almasihu shine Dan Allah.”
38 Mandó parar el carruaje. Ambos bajaron al agua, y Felipe lo bautizó.
Sai Bahabashen ya umarta a tsai da karussar. Sai suka zo wurin ruwa dukan su biyu, Filibus da baban, Filibus kuwa yayi masa baftisma.
39 Cuando subieron del agua, [el] Espíritu del Señor arrebató a Felipe, y el eunuco no lo vio más, pero siguió su camino con gozo.
Yayin da suka fito daga cikin ruwan, Ruhun Ubangiji ya dauke Filibus; baban bai sake ganin shi ba, sai ya ci gaba da tafiyar sa yana murna.
40 Felipe se halló en Azoto, y al pasar, proclamaba las Buenas Noticias a todas las ciudades, hasta llegar a Cesarea.
Amma Filibus ya bayyana a Azotus. Ya ratsa wannan yankin yana wa'azin bishara a dukan garuruwan, har sa'anda ya iso Kaisariya.

< Hechos 8 >