< 1 Pedro 1 >

1 Pedro, un apóstol de Jesucristo, a [los] peregrinos elegidos de una diáspora en Ponto, Galacia, Capadocia, Asia y Bitinia,
Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya.
2 [elegidos] según [la] presciencia de Dios Padre en santificación del Espíritu, para que le obedecieran y fueran rociados con [la ]sangre de Jesucristo. Gracia y paz se les concedan abundantemente.
Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.
3 Bendito el Dios y Padre de nuestro Señor Jesucristo, Quien según su gran misericordia causó que renaciéramos para una esperanza viva por medio de [la] resurrección de Jesucristo de entre [los] muertos,
Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
4 para [la] herencia incorruptible, incontaminada e inmarchitable, reservada en los cielos para ustedes.
Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku.
5 Por [el] poder de Dios ustedes son protegidos bajo custodia por medio de [la] fe para [la] salvación preparada, a fin de que [les ]sea manifestada en [el] tiempo final.
Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.
6 Esto es un gran gozo para ustedes, aunque ahora, si es necesario, por poco tiempo sean afligidos con diversas pruebas.
Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri.
7 La fe es más preciosa que el oro, el cual, aunque perecedero, se prueba con fuego. La prueba de su fe debe resultar en alabanza, gloria y honra en [la] aparición de Jesucristo,
Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.
8 a Quien aman, aunque no [lo] vean, en Quien creen sin verlo ahora. Se alegran con un gozo indecible y esplendoroso,
Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka.
9 y obtienen el fin de su fe: [la] salvación de sus almas.
Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku.
10 Los profetas que profetizaron con respecto a la gracia para ustedes, escudriñaron e indagaron cuidadosamente en cuanto a esta salvación.
Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.
11 Investigaron quién y cual tiempo indicaba el Espíritu de Cristo que estaba en ellos, el cual anunciaba con anticipación los padecimientos de Cristo y los resultados gloriosos que vendrían después de ellos.
Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya.
12 A ellos se les reveló que no administraban esto para ellos mismos sino para ustedes. Tales cosas les fueron anunciadas por los que predicaron estas Buenas Noticias según [el] Espíritu Santo enviado del cielo. Los ángeles anhelan mirar esto.
An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.
13 Por tanto átense el cinturón de su entendimiento. Sean sobrios. Esperen por completo la gracia que se les traerá cuando se manifieste Jesucristo.
Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu.
14 Como hijos obedientes, no se amolden a las antiguas pasiones que tenían en su ignorancia.
Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.
15 El que los llamó es santo. Sean también ustedes santos en toda su manera de vivir.
Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku.
16 Porque está escrito: Me serán santos, porque Yo soy santo.
Domin a rubuce yake, “Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne.”
17 Si invocan como Padre al que juzga con imparcialidad según la obra de cada uno, pórtense con temor todo el tiempo de su peregrinación.
Idan ku na kira bisa gare shi “Uba” shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.
18 Porque saben que fueron rescatados de su vana manera de vivir, heredada de sus antepasados, no con cosas corruptibles, como oro o plata,
Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku.
19 sino con la sangre preciosa de Cristo, como Cordero sin mancha y sin defecto,
Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.
20 ciertamente escogido antes de la fundación del mundo, pero manifestado en los últimos tiempos por amor a ustedes,
An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku.
21 los que por medio de Él son fieles a Dios, Quien lo resucitó de entre [los] muertos y le dio gloria para que su fe y esperanza estén en Dios.
Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.
22 Puesto que ustedes purificaron sus almas por la obediencia a la verdad para [el] amor fraternal no fingido, ámense los unos a los otros fervientemente de corazón.
Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya.
23 No renacieron de una simiente corruptible, sino incorruptible, por medio de [la] Palabra de Dios, que vive y permanece para siempre. (aiōn g165)
da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama. (aiōn g165)
24 Porque: Toda carne es como hierba, Y todo su esplendor como [la ]flor de hierba. La hierba se marchita y la flor se cae.
Gama “dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi,
25 Pero la Palabra del Señor permanece para siempre. Ésta es la Palabra que se les predicó a ustedes por medio de las Buenas Noticias. (aiōn g165)
amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. “Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta.” (aiōn g165)

< 1 Pedro 1 >