< 1 Corintios 14 >

1 Sigan el amor y procuren los dones espirituales, pero sobre todo que profeticen.
Ku dafkaci kauna kuma ku himmatu domin baye bayen ruhaniya, musamman domin kuyi anabci.
2 El que habla en lenguas, habla a Dios, no a los hombres, porque nadie [lo] entiende, pues en [su] espíritu habla misterios.
Domin wanda yake magana da harshe bada mutane yake magana ba amma da Allah. domin babu mai fahimtarsa saboda yana zancen boyayyun abubuwa ciki Ruhu.
3 Pero el que profetiza, habla a [los] hombres para edificación, exhortación y consolación.
Amma wanda yake anabci da mutane yake magana domin ya gina su, ya karfafa su, kuma ya ta'azantar dasu.
4 El que habla en lenguas se edifica él mismo, pero el que profetiza edifica a [la] iglesia.
Wanda yake magana da wani harshe, kansa yake ginawa, amma mai yin annabci kuwa, ikilisiya yake ginawa.
5 Entonces deseo que todos ustedes hablen en lenguas, pero más que profeticen, pues mayor es el que profetiza que el que habla en lenguas, a menos que interprete para que la iglesia sea edificada.
To, fatana ace dukan ku kuna magana da harsuna. Amma fiye da hakama, fatana ace kuyi anabci. Wanda yake anabci yafi wanda yake magana da harsuna ( sai dai idan wani ya fassara domin ikilisiya ta ginu).
6 Ahora, hermanos, si los visito y hablo en lenguas, ¿qué les aprovecharía si no les hablo con revelación, conocimiento, profecía o enseñanza?
Amma yanzu, 'yan'uwa, in na zo wurin ku ina magana da harsuna, ta yaya zaku karu dani? ba zaya yiwu ba, sai idan nayi maku magana da wahayi, ko sani, ko anabci, ko koyarwa.
7 Aun las cosas inanimadas que dan sonido, como la flauta o el arpa, si no producen sonidos distintos, ¿cómo se sabrá lo que se toca con la flauta o se tañe con el arpa?
Idan kayan kida marasa rai suna fitar da sauti - kamar su sarewa da algaita - kuma basu fitar da amo daban daban, ta yaya wani zaya san irin amon da sarewar da algaitar suke kadawa?
8 De igual manera, si una trompeta no da sonido claro, ¿quién se prepararía para la batalla?
Domin idan aka busa kaho da sauti marar ma'ana, ta yaya wani zaya san lokacin da ya dace ya shirya zuwa yaki?
9 Así también ustedes, si por medio de la lengua no dan palabra fácilmente comprensible, ¿cómo entenderán lo que se habla? Porque hablarían al aire.
Haka yake game da ku. Idan kuka furta zance marar ma'ana, ta yaya wani zaya fahimci abinda kukace? zaku yita magana, kuma babu wanda zaya fahimce ku.
10 Sin duda, ¡cuántas clases de lenguas hay en el mundo, y ninguna carece de significado!
Babu shakka akwai harsuna daban daban a duniya, kuma babu wanda baya da ma'ana.
11 Si, pues, no entiendo el significado de las palabras, seré un extranjero para el que habla, y el que habla, un extranjero para mí.
Amma idan ban san ma'anar wani harshe ba, zan zama bare ga mai maganar, kuma mai maganar zaya zama bare a gareni.
12 Así también ustedes, puesto que anhelan [dones] espirituales, procuren abundar para la edificación de la iglesia.
haka yake gare ku. Tun da kuna da dokin bayyanuwar Ruhu, ku himmatu da habaka cikin gina ikilisiya.
13 Por tanto, el que habla en lengua, hable con Dios para que interprete.
To wanda yake magana da harshe yayi addu'a domin ya iya fassarawa.
14 Cuando hablo con Dios en una lengua, mi espíritu comunica, pero mi entendimiento queda sin provecho.
Domin idan nayi addu'a da harshe, ruhuna yayi addu'a, amma fahimtata bata karu ba.
15 ¿Entonces, qué [digo]? Hablaré con Dios con el espíritu, pero también hablaré con el entendimiento. Cantaré alabanza con el espíritu, pero también cantaré con el entendimiento.
To, me zan yi? Zan yi addu'a da ruhuna, in kuma yi addu'a da fahimtata. Zan yi raira waka da ruhuna, kuma in raira waka da fahimtata.
16 De otra manera, cuando bendigas en espíritu, el que quiere entender, ¿cómo dirá amén a tu acción de gracias si no sabe [lo] que dices?
In ba haka ba, idan ka yi yabon Allah da ruhu kawai, ta yaya wanda yake waje zai ce, “Amin” a kan godiyar da kake yi in bai san abin da kake fada ba?
17 Porque tú, ciertamente, expresas bien la acción de gracias, pero el otro no es edificado.
Babu shakka kayi godiya sosai, amma wanin baya ginu ba.
18 Doy gracias a Dios que hablo en lenguas más que todos ustedes,
Nagodewa Allah ina magana da harsuna fiye da ku duka.
19 pero en la iglesia prefiero hablar cinco palabras con mi entendimiento para instruir también a otros, que 10.000 palabras en lengua desconocida.
Duk da haka dai a taron ikilisiya na gwammace in yi magana da kalmomi biyar cikin fahimta saboda inganta wadansu fiye da dubu goma da harshe.
20 Hermanos, no sean niños en el entendimiento. Sean niños en la perversidad, pero maduros en el entendimiento.
'Yan'uwa, kada ku zama yara cikin tunani, sai dai a wajen aikin mugunta, ku yi halin jarirai, amma a tunaninku ku girma.
21 En la Ley está escrito: Hablaré a este pueblo en lenguas extrañas y por medio de otros. Ni aun así me escucharán, dice el Señor.
A rubuce yake a shari'a cewa, “zan yi magana da mutanen nan ta wurin mutane masu bakin harsuna, da kuma lebunan baki. Duk da haka kuwa ba za su saurare ni ba”, in ji Ubangiji.
22 Por tanto, las lenguas no son señal para los que creen, sino para los incrédulos. Pero profetizar no [es señal] para los incrédulos, sino para los que creen.
Amma harsuna alamu ne, ba ga masu bada gaskiya ba, sai dai ga marasa ba da gaskiya. Annabci kuwa alama ce ga masu ba da gaskiya, amma ba don marasa bangaskiya ba.
23 De manera que si toda la iglesia se congrega en un lugar y todos hablan en lenguas, y entran unos incrédulos o unos que no tienen [ese] don, ¿no dirán que están locos?
Saboda haka, in dukan ikilisiya ta taru, kowa kuwa yana magana da wasu harsuna, wadansu na waje da kuma marasa ba da gaskiya suka shigo, ashe, ba sai su ce kun haukace ba ba?
24 Pero si todos profetizan y entra algún incrédulo que quiere entender, queda expuesto, llamado a cuentas por todos.
In kuwa kowa yana yin annabci, wani kuma marar ba da gaskiya ko wani daga waje ya shigo, maganar kuwa zata ratsa shi. Za a ma hukanta shi a kan maganar,
25 Los secretos de su corazón son manifiestos, y así se postrará sobre el rostro, adorará a Dios y confesará que Dios está verdaderamente entre ustedes.
asiran zuciyarsa kuma za su tonu. Sakamokon haka, sai ya fadi ya yi wa Allah sujada, zaya furta cewa lallai Allah yana tare da ku.
26 ¿Entonces, hermanos, qué [significa esto]? Cuando se reúnan, cada uno tiene salmo, enseñanza, revelación, lengua o interpretación. Hagan todo para edificación.
Sai me kuma 'yan'uwa? idan kuka tattaru, wani yana da zabura, koyarwa, wahayi, harshe, ko fassara. Kuyi komai domin gina ikilisiya.
27 Si se habla en lengua, que sean dos, o a lo más tres, y uno después de otro, y uno interprete.
Idan wani yayi magana da harshe, bari a sami mutum biyu ko uku a yawansu, kuma kowa yayi daya bayan daya. Sai wani ya fassara abinda aka fada.
28 Cuando no haya intérprete, calle en [la] iglesia. Hable para él mismo y a Dios.
Amma idan babu wanda zaya fassara, bari dukansu suyi shiru a ikilisiya. Bari kowa yayi wa kansa maganar a gida shi kadai da kuma Allah.
29 Hablen dos o tres profetas, y los demás evalúen.
Bari annabawa biyu ko uku suyi magana, bari sauran su saurara tare da bambance abinda ake fada.
30 Si a otro que está sentado se le revela [algo], calle el primero.
Idan kuma anba wani fahimta wanda yana zaune a cikin sujadar, bari wanda yake ta magana kafin yanzu yayi shiru.
31 Porque todos pueden hablar uno por uno, para que todos aprendan y sean exhortados.
Dukanku kuna iya yin annabci daya bayan daya, domin kowannen ku yayi koyi, a kuma samu karfafawa.
32 Los espíritus de los profetas están subordinados a los profetas.
Gama ruhohin annabawa suna karkashin annabawa,
33 Porque Dios no es de desorden, sino de paz. Como en todas las iglesias de los santos,
domin Allah ba Allahn rudu ba ne, na salama ne. Haka yake kuwa a duk ikllisiyoyin masu bangaskiya.
34 las mujeres callen en las congregaciones, porque no les es permitido hablar. Sean obedientes, como también dice la Ley.
Mataye suyi shiru a ikilisiyoyi. Domin ba a basu dama ba suyi magana. A maimako, su zama masu sadaukar da kansu, kamar yadda doka ta ce.
35 Si quieren aprender algo, pregunten en casa a sus esposos, porque es impropio que una mujer hable en la congregación.
Idan akwai abinda suke so su koya, bari su tambayi mazajen su a gida. Domin abin kunya ne mace tayi magana a ikilisiya.
36 ¿Salió de ustedes la Palabra de Dios, o solo llegó a ustedes?
Daga wurinku maganar Allah ta zo ne? ko kuwa a gare ku kadai ta iso?
37 Si alguno supone que es profeta o espiritual, reconozca las cosas que les escribo, porque es Mandamiento del Señor.
In wani yana zaton shi ma annabi ne, ko kuwa mai ruhaniya, to, sai ya fahimta, abin nan da nake rubuta maku umarni ne daga wurin Ubangiji.
38 Pero si alguno hace caso omiso, que sea ignorado.
In kuwa wani ya ki kula da wannan, shi ma kada a kula da shi.
39 Así que, hermanos, procuren profetizar. No impidan hablar en lenguas.
Saboda haka, 'yan'uwa, ku yi marmarin yin annabci sosai, sa'an nan kada ku hana kow yin magana da harsuna.
40 Pero hagan todo decentemente y con orden.
Sai dai a yi komai ta hanyar da ta dace bisa ga tsari.

< 1 Corintios 14 >