< 1 Crónicas 15 >
1 David hizo para él casas en la Ciudad de David. Preparó un lugar para el Arca de ʼElohim y levantó una tienda para ella.
Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
2 Entonces David dijo: El Arca de ʼElohim no debe ser llevada sino por los levitas, porque Yavé los eligió para que la lleven y le sirvan perpetuamente.
Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
3 David congregó a todo Israel en Jerusalén para que trasladaran el Arca de Yavé al lugar que había preparado para ella.
Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
4 David reunió a los hijos de Aarón y a los levitas:
Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
5 De los hijos de Coat, Uriel el principal y 120 de sus hermanos.
Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
6 De los hijos de Merari, Asaías el principal, y 229 de sus hermanos.
daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
7 De los hijos de Gersón, Joel el principal, y 130 de sus hermanos.
daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
8 De los hijos de Elizafán: Semaías el principal, y 200 de sus hermanos.
daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
9 De los hijos de Hebrón, Eliel el principal, y 80 de sus hermanos.
daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
10 De los hijos de Uziel, Aminadab el principal, y 112 de sus hermanos.
daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
11 David llamó a los sacerdotes Sadoc y Abiatar, y a los levitas Uriel, Asaías, Joel, Semaías, Eliel y Aminadab.
Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
12 Les dijo: Ustedes son los principales padres de las familias de los levitas. Santifíquense, ustedes y sus hermanos, para que suban el Arca de Yavé ʼElohim de Israel al lugar que le preparé.
Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
13 Pues por no hacerlo ustedes la primera vez, Yavé nuestro ʼElohim nos quebrantó, por cuanto no le consultamos según el orden prescrito.
Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
14 Así que los sacerdotes y los levitas se santificaron para subir el Arca de Yavé ʼElohim de Israel.
Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
15 Los hijos de los levitas llevaron el Arca de ʼElohim con las barras puestas sobre sus hombros, tal como Moisés ordenó, según la Palabra de Yavé.
Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
16 Asimismo David dijo a los jefes de los levitas que designaran de sus hermanos cantores con instrumentos de música, con salterios y arpas y címbalos resonantes, y que alzaran la voz con alegría.
Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
17 Los levitas designaron a Hemán, hijo de Joel, y de sus parientes a Asaf, hijo de Berequías, y de los hijos de Merari y de sus hermanos, a Etán, hijo de Cusaías.
Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
18 Con ellos, a sus hermanos de segundo grado, a Zacarías, hijo de Jahaziel, Semiramot, Jehiel, Unni, Eliab, Benaía, Maasías, Matatías, Elifelehu, Micnías, Obed-edom y Jeiel, los porteros.
Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
19 Así Hemán, Asaf y Etán, que eran cantores, sonaban címbalos de bronce.
Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
20 Zacarías, Aziel, Semiramot, Jehiel, Uni, Eliab, Maasías y Benaía, tocaban salterios de tono alto.
Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
21 Matatías, Elifelehu, Micnías, Obede-dom, Jeiel y Azazías, dirigían con liras templadas en tono alto.
Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
22 Quenanías, principal de los levitas en la música, fue designado para elevar el canto, porque era entendido para esto.
Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
23 Berequías y Elcana eran porteros del Arca.
Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
24 Sebanías, Josafat, Natanael, Amasai, Zacarías, Benaía y Eliezer, sacerdotes, tocaban las trompetas delante del Arca de ʼElohim, y Obed-edom y Jehías eran también porteros del Arca.
Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
25 Entonces David fue con los ancianos de Israel y los jefes de millares a subir el Arca del Pacto de Yavé con alegría, desde la casa de Obed-edom.
Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
26 Sucedió que como ʼElohim ayudaba a los levitas que llevaban el Arca del Pacto de Yavé, ellos sacrificaron siete becerros y siete carneros.
Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
27 David iba vestido con un manto de lino fino y también los cantores y todos los levitas que cargaban el Arca. Quenanías era el director del canto de los cantores. David llevaba sobre él un efod de lino.
To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
28 De esta manera todo Israel subía el Arca del Pacto de Yavé con aclamaciones al sonido de la corneta, con trompetas y címbalos muy resonantes y al son de salterios y arpas.
Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
29 Cuando el Arca del Pacto de Yavé entró en la Ciudad de David, aconteció que Mical, la hija de Saúl, miró por la ventana. Al ver que el rey David saltaba y se regocijaba, lo despreció en su corazón.
Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.