< Salmos 96 >
1 ¡Cantad a Yahvé un cántico nuevo! Cantad a Yahvé, toda la tierra.
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
2 ¡Canta a Yahvé! ¡Bendito sea su nombre! ¡Proclama su salvación de día en día!
Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
3 Anuncia su gloria entre las naciones, sus obras maravillosas entre todos los pueblos.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
4 Porque Yahvé es grande y digno de gran alabanza. Debe ser temido por encima de todos los dioses.
Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
5 Porque todos los dioses de los pueblos son ídolos, pero Yahvé hizo los cielos.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
6 El honor y la majestad están ante él. La fuerza y la belleza están en su santuario.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
7 Atribúyanse a Yahvé, familias de naciones, atribuir a Yahvé la gloria y la fuerza.
Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
8 Atribuye a Yahvé la gloria que merece su nombre. Traed una ofrenda y venid a sus atrios.
Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
9 Adoren a Yahvé en forma sagrada. Temblad ante él, toda la tierra.
Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
10 Di entre las naciones: “Yahvé reina”. El mundo también está establecido. No se puede mover. Él juzgará a los pueblos con equidad.
Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
11 Que se alegren los cielos y se regocije la tierra. ¡Que el mar ruge, y su plenitud!
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
12 ¡Que el campo y todo lo que hay en él se alegre! Entonces todos los árboles del bosque cantarán de alegría
bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
13 delante de Yahvé; porque él viene, porque viene a juzgar la tierra. Él juzgará al mundo con justicia, los pueblos con su verdad.
za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.