< Salmos 9 >

1 Para el músico jefe. Ajustado a “La Muerte del Hijo”. Un salmo de David. Daré gracias a Yahvé de todo corazón. Contaré todas tus obras maravillosas.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
2 Me alegraré y me regocijaré en ti. Cantaré alabanzas a tu nombre, oh Altísimo.
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
3 Cuando mis enemigos se vuelvan, tropiezan y perecen en tu presencia.
Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
4 Porque has mantenido mi causa justa. Te sientas en el trono juzgando con justicia.
Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
5 Has reprendido a las naciones. Has destruido a los malvados. Has borrado su nombre para siempre.
Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
6 El enemigo se ve superado por una ruina sin fin. El propio recuerdo de las ciudades que habéis derribado ha perecido.
Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
7 Pero Yahvé reina para siempre. Ha preparado su trono para el juicio.
Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
8 Él juzgará al mundo con justicia. Administrará el juicio a los pueblos con rectitud.
Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
9 Yahvé también será una torre alta para los oprimidos; una torre alta en tiempos de problemas.
Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
10 Los que conocen tu nombre pondrán su confianza en ti, porque tú, Yahvé, no has abandonado a los que te buscan.
Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
11 Canten alabanzas a Yahvé, que habita en Sión, y declarar entre el pueblo lo que ha hecho.
Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
12 Porque el que venga la sangre se acuerda de ellos. No olvida el clamor de los afligidos.
Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
13 Ten piedad de mí, Yahvé. Mira mi aflicción por los que me odian, y sácame de las puertas de la muerte,
Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
14 para que pueda mostrar todas tus alabanzas. Me alegraré de tu salvación en las puertas de la hija de Sión.
don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
15 Las naciones se han hundido en el pozo que hicieron. En la red que escondieron, su propio pie es tomado.
Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
16 Yahvé se ha dado a conocer. Ha ejecutado la sentencia. El malvado es atrapado por la obra de sus propias manos. Meditación. (Selah)
An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
17 Los impíos serán devueltos al Seol, incluso todas las naciones que se olvidan de Dios. (Sheol h7585)
Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
18 Porque el necesitado no será siempre olvidado, ni la esperanza de los pobres perecerá para siempre.
Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
19 ¡Levántate, Yahvé! No dejes que el hombre prevalezca. Que las naciones sean juzgadas a tus ojos.
Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
20 Ponen temor, Yahvé. Que las naciones sepan que sólo son hombres. (Selah)
Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)

< Salmos 9 >