< Salmos 88 >
1 Una canción. Un Salmo de los hijos de Coré. Para el músico principal. Con la melodía de “El sufrimiento de la aflicción”. Una contemplación de Hemán, el ezraíta. Yahvé, el Dios de mi salvación, He llorado día y noche ante ti.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Deja que mi oración entre en tu presencia. Poner el oído en mi grito.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 Porque mi alma está llena de problemas. Mi vida se acerca al Seol. (Sheol )
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
4 Me cuentan entre los que bajan a la fosa. Soy como un hombre que no tiene ayuda,
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 apartada entre los muertos, como los muertos que yacen en la tumba, de quien ya no te acuerdas. Están cortados de su mano.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Me has puesto en el pozo más bajo, en las profundidades más oscuras.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Tu ira pesa sobre mí. Me has afligido con todas tus olas. (Selah)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Me has quitado a mis amigos. Me has convertido en una abominación para ellos. Estoy confinado y no puedo escapar.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mis ojos están oscurecidos por el dolor. Te he invocado a diario, Yahvé. He extendido mis manos hacia ti.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 ¿Muestra usted maravillas a los muertos? ¿Los espíritus difuntos se levantan y te alaban? (Selah)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 ¿Se declara tu bondad en la tumba? ¿O su fidelidad en la Destrucción?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 ¿Se dan a conocer tus maravillas en la oscuridad? ¿O tu justicia en la tierra del olvido?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Pero a ti, Yahvé, he clamado. Por la mañana, mi oración se presenta ante ti.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Yahvé, ¿por qué rechazas mi alma? ¿Por qué me ocultas la cara?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Estoy afligido y dispuesto a morir desde mi juventud. Mientras sufro tus terrores, me distraigo.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Tu ira feroz ha pasado por encima de mí. Tus terrores me han aislado.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Venían a mi alrededor como el agua durante todo el día. Me envolvieron por completo.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Has puesto lejos de mí al amante y al amigo, y mis amigos en la oscuridad.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.