< Salmos 78 >

1 Una contemplación de Asaf. Escuchad mi enseñanza, pueblo mío. Vuelve tus oídos a las palabras de mi boca.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Voy a abrir mi boca en una parábola. Pronunciaré oscuros refranes de antaño,
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 que hemos oído y conocido, y nuestros padres nos lo han dicho.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 No los esconderemos de sus hijos, contar a la generación venidera las alabanzas de Yahvé, su fuerza y las maravillas que ha hecho.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Porque estableció un pacto en Jacob, y designó una enseñanza en Israel, que ordenó a nuestros padres, que los den a conocer a sus hijos;
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 para que la generación venidera lo sepa, incluso los niños que han de nacer; que deben levantarse y decírselo a sus hijos,
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 para que pongan su esperanza en Dios, y no olvidar las obras de Dios, sino que guarden sus mandamientos,
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 y que no sean como sus padres — una generación obstinada y rebelde, una generación que no ha fidelizado su corazón, cuyo espíritu no estaba firme con Dios.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Los hijos de Efraín, armados y con arcos, se volvió atrás en el día de la batalla.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 No cumplieron el pacto de Dios, y se negó a caminar en su ley.
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Se olvidaron de sus actos, sus maravillosas hazañas que les había mostrado.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Hizo cosas maravillosas a la vista de sus padres, en la tierra de Egipto, en el campo de Zoan.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Partió el mar y los hizo pasar. Hizo que las aguas se mantuvieran como un montón.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 De día también los guiaba con una nube, y toda la noche con una luz de fuego.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Partió rocas en el desierto, y les dio de beber abundantemente como de las profundidades.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 También sacó arroyos de la roca, e hizo que las aguas corrieran como ríos.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Sin embargo, siguieron pecando contra él, para rebelarse contra el Altísimo en el desierto.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 Tentaron a Dios en su corazón pidiendo comida según su deseo.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Sí, hablaron contra Dios. Dijeron: “¿Puede Dios preparar una mesa en el desierto?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 He aquí que golpeó la roca, de modo que las aguas brotaron, y los arroyos se desbordaron. ¿Puede dar pan también? ¿Proporcionará carne a su pueblo?”
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Por lo tanto, Yahvé escuchó y se enojó. Se encendió un fuego contra Jacob, La ira también se dirigió contra Israel,
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 porque no creían en Dios, y no confió en su salvación.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Sin embargo, él mandaba en los cielos, y abrió las puertas del cielo.
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 Hizo llover maná sobre ellos para que comieran, y les dio comida del cielo.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 El hombre comió el pan de los ángeles. Les mandó comida hasta la saciedad.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Hizo que el viento del este soplara en el cielo. Con su poder guió el viento del sur.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 También hizo llover sobre ellos carne como el polvo, aves aladas como la arena de los mares.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 Los dejó caer en medio de su campamento, alrededor de sus viviendas.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Comieron, pues, y se saciaron. Les dio su propio deseo.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 No se apartaron de sus antojos. La comida aún estaba en sus bocas,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 cuando la ira de Dios subió contra ellos, mató a algunos de sus más fuertes, y abatió a los jóvenes de Israel.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 A pesar de todo esto, pecaron, y no creían en sus maravillosas obras.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Por eso consumió sus días en la vanidad, y sus años de terror.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Cuando los mató, entonces preguntaron por él. Volvieron y buscaron a Dios con ahínco.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 Recordaron que Dios era su roca, el Dios Altísimo, su redentor.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Pero ellos lo halagaron con su boca, y le mintieron con la lengua.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 Porque su corazón no estaba bien con él, ni fueron fieles a su pacto.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Pero él, siendo misericordioso, perdonó la iniquidad y no los destruyó. Sí, muchas veces desvió su ira, y no despertó toda su ira.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Recordó que no eran más que carne, un viento que pasa y no vuelve.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Cuántas veces se rebelaron contra él en el desierto, ¡y lo afligió en el desierto!
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 Se volvieron y tentaron a Dios, y provocó al Santo de Israel.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 No se acordaron de su mano, ni el día en que los redimió del adversario;
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 cómo puso sus signos en Egipto, sus maravillas en el campo de Zoan,
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 convirtió sus ríos en sangre, y sus arroyos, para que no pudieran beber.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Envió entre ellos enjambres de moscas, que los devoraron; y ranas, que los destruyeron.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 También le dio su aumento a la oruga, y su trabajo a la langosta.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Destruyó sus vides con el granizo, sus higueras de sicomoro con la escarcha.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 También entregó su ganado al granizo, y sus rebaños a los rayos calientes.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Arrojó sobre ellos la ferocidad de su ira, la ira, la indignación y los problemas, y una banda de ángeles del mal.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Hizo un camino para su ira. No les perdonó el alma de la muerte, sino que entregaron su vida a la peste,
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 y golpeó a todos los primogénitos de Egipto, el jefe de su fuerza en las tiendas de Cam.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Pero sacó a los suyos como a ovejas, y los guió en el desierto como un rebaño.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Los condujo con seguridad, para que no tuvieran miedo, pero el mar arrolló a sus enemigos.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Los llevó a la frontera de su santuario, a esta montaña, que su mano derecha había tomado.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 También expulsó a las naciones que estaban delante de ellos, les asignó una herencia por línea, e hizo que las tribus de Israel habitasen en sus tiendas.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Sin embargo, tentaron y se rebelaron contra el Dios Altísimo, y no mantuvo sus testimonios,
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 sino que se volvieron atrás, y actuaron con traición como sus padres. Estaban retorcidos como un arco engañoso.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Porque lo provocaron a la ira con sus lugares altos, y lo movieron a los celos con sus imágenes grabadas.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Cuando Dios escuchó esto, se enojó, y aborrecía enormemente a Israel,
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 por lo que abandonó la tienda de Silo, la tienda que colocó entre los hombres,
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 y entregó su fuerza al cautiverio, su gloria en la mano del adversario.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 También entregó a su pueblo a la espada, y se enfadó con su herencia.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 El fuego devoró a sus jóvenes. Sus vírgenes no tenían canción de boda.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Sus sacerdotes cayeron por la espada, y sus viudas no podían llorar.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Entonces el Señor se despertó como quien sale del sueño, como un hombre poderoso que grita a causa del vino.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 Golpeó a sus adversarios hacia atrás. Los sometió a un reproche perpetuo.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Además, rechazó la tienda de José, y no eligió la tribu de Efraín,
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Pero eligió la tribu de Judá, El Monte Sión que él amaba.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Construyó su santuario como las alturas, como la tierra que ha establecido para siempre.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 También eligió a David, su siervo, y lo sacaron de los rediles;
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 de seguir a las ovejas que tienen sus crías, lo llevó a ser el pastor de Jacob, su pueblo, e Israel, su herencia.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Así quefue su pastor según la integridad de su corazón, y los guió con la destreza de sus manos.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Salmos 78 >