< Salmos 75 >

1 Para el músico jefe. Con la melodía de “No destruyas”. Un salmo de Asaf. Una canción. Te damos gracias, Dios. Damos gracias, porque tu Nombre está cerca. Los hombres cuentan tus obras maravillosas.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
2 Cuando elijo la hora señalada, Yo juzgaré sin culpa.
Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
3 La tierra y todos sus habitantes tiemblan. Sostengo firmemente sus pilares. (Selah)
Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
4 Dije a los arrogantes: “¡No te jactes!” Les dije a los malvados: “No levanten el cuerno.
Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
5 No levantes tu cuerno en alto. No hables con el cuello rígido”.
Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
6 Porque ni desde el este, ni desde el oeste, ni aún del sur, viene la exaltación.
Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
7 Pero Dios es el juez. Deja a uno y levanta a otro.
Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
8 Porque en la mano de Yahvé hay una copa, lleno de vino espumoso mezclado con especias. Lo vierte. En efecto, los malvados de la tierra beben y se lo beben hasta las heces.
A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
9 Pero yo lo declararé para siempre: Cantaré alabanzas al Dios de Jacob.
Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
10 Cortaré todos los cuernos de los malvados, pero los cuernos de los justos serán levantados.
wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”

< Salmos 75 >