< Salmos 74 >
1 Una contemplación de Asaf. Dios, ¿por qué nos has rechazado para siempre? ¿Por qué arde tu ira contra las ovejas de tu prado?
Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
2 Acuérdate de tu congregación, que adquiriste desde antaño, que has redimido para ser la tribu de tu herencia: Monte Sion, en el que has vivido.
Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
3 Levanta tus pies hacia las ruinas perpetuas, todo el mal que el enemigo ha hecho en el santuario.
Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
4 Tus adversarios han rugido en medio de tu asamblea. Han establecido sus normas como señales.
Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
5 Se comportaron como hombres que empuñan hachas, cortando un matorral de árboles.
Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
6 Ahora rompen toda su obra tallada con hachas y martillos.
Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
7 Han quemado tu santuario hasta los cimientos. Han profanado la morada de tu Nombre.
Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
8 Dijeron en su corazón: “Los aplastaremos por completo”. Han quemado todos los lugares de la tierra donde se adoraba a Dios.
Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
9 No vemos signos milagrosos. Ya no hay ningún profeta, tampoco hay entre nosotros nadie que sepa cuánto tiempo.
Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
10 ¿Hasta cuándo, Dios, reprochará el adversario? ¿El enemigo blasfemará tu nombre para siempre?
Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
11 ¿Por qué retiras tu mano, incluso tu mano derecha? ¡Sácalo de tu pecho y consúmelos!
Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
12 Sin embargo, Dios es mi Rey de antaño, obrando la salvación en toda la tierra.
Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
13 Dividiste el mar con tu fuerza. Rompiste las cabezas de los monstruos marinos en las aguas.
Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
14 Rompiste las cabezas del Leviatán en pedazos. Lo diste como alimento a la gente y a las criaturas del desierto.
Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
15 Abriste el manantial y el arroyo. Has secado ríos caudalosos.
Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
16 El día es tuyo, la noche también. Has preparado la luz y el sol.
Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
17 Tú has fijado todos los límites de la tierra. Has hecho el verano y el invierno.
Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
18 Acuérdate de esto: el enemigo se ha burlado de ti, Yahvé. Los insensatos han blasfemado tu nombre.
Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
19 No entregues el alma de tu paloma a las fieras. No olvides la vida de tus pobres para siempre.
Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
20 Honra tu pacto, porque las guaridas de la violencia llenan los lugares oscuros de la tierra.
Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
21 No dejes que los oprimidos vuelvan avergonzados. Que los pobres y los necesitados alaben tu nombre.
Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
22 ¡Levántate, Dios! Defiende tu propia causa. Recuerda cómo el tonto se burla de ti todo el día.
Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
23 No olvides la voz de tus adversarios. El tumulto de los que se levantan contra ti asciende continuamente.
Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.