< Salmos 59 >

1 Para el músico jefe. Con la melodía de “No destruyas”. Un poema de David, cuando Saúl mandó, y vigilaron la casa para matarlo. Líbrame de mis enemigos, Dios mío. Ponme en alto de los que se levantan contra mí.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
2 Líbrame de los obreros de la iniquidad. Sálvame de los hombres sedientos de sangre.
Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
3 Porque, he aquí, ellos acechan mi alma. Los poderosos se reúnen contra mí, no por mi desobediencia, ni por mi pecado, Yahvé.
Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
4 No he hecho nada malo, pero están dispuestos a atacarme. ¡Levántate, mira, y ayúdame!
Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
5 Tú, Yahvé Dios de los Ejércitos, el Dios de Israel, despierta para castigar a las naciones. No tengas piedad de los malvados traidores. (Selah)
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
6 Regresan al atardecer, aullando como perros, y merodean por la ciudad.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
7 He aquí que vomitan con la boca. Las espadas están en sus labios, “Porque”, dicen, “¿quién nos escucha?”
Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
8 Pero tú, Yahvé, te ríes de ellos. Te burlas de todas las naciones.
Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
9 Oh, mi Fuerza, yo velo por ti, porque Dios es mi alta torre.
Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
10 Mi Dios irá delante de mí con su amorosa bondad. Dios me permitirá mirar a mis enemigos con triunfo.
Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
11 No los mates, o mi pueblo se olvidará. Dispérsalos con tu poder y derríbalos, Señor, nuestro escudo.
Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
12 Por el pecado de su boca y las palabras de sus labios, que se dejen atrapar por su orgullo, por las maldiciones y mentiras que pronuncian.
Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
13 Consúmelos con ira. Consúmelos y ya no existirán. Hazles saber que Dios gobierna en Jacob, hasta los confines de la tierra. (Selah)
ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
14 Al anochecer, que vuelvan. Que aúllen como un perro y recorran la ciudad.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
15 Andarán de un lado a otro en busca de comida, y esperar toda la noche si no están satisfechos.
Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
16 Pero yo cantaré tu fuerza. Sí, cantaré en voz alta tu amorosa bondad por la mañana. Porque tú has sido mi alta torre, un refugio en el día de mi angustia.
Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
17 A ti, mi fuerza, te cantaré alabanzas. Porque Dios es mi alta torre, el Dios de mi misericordia.
Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.

< Salmos 59 >