< Salmos 55 >

1 Para el músico jefe. Sobre los instrumentos de cuerda. Una contemplación de David. Escucha mi oración, Dios. No te escondas de mi súplica.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Atiéndeme y respóndeme. Estoy inquieto en mi queja, y gime
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 por la voz del enemigo, a causa de la opresión de los malvados. Porque me hacen sufrir. Con rabia me guardan rencor.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 Mi corazón está gravemente dolorido en mi interior. Los terrores de la muerte han caído sobre mí.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 El temor y el temblor se han apoderado de mí. El horror me ha abrumado.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 Dije: “¡Oh, si tuviera alas como una paloma! Entonces volaría y descansaría.
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 He aquí que entonces me alejaría. Me alojaría en el desierto”. (Selah)
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 “Me apresuraría a refugiarme del viento tempestuoso y de la tormenta”.
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Confúndelos, Señor, y confunde su lenguaje, porque he visto violencia y lucha en la ciudad.
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 Día y noche merodean por sus muros. La malicia y el abuso también están en ella.
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 Las fuerzas destructivas están dentro de ella. Las amenazas y las mentiras no salen de sus calles.
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 Porque no fue un enemigo quien me insultó, entonces podría haberlo soportado. Tampoco el que me odiaba se levantó contra mí, entonces me habría escondido de él.
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 Pero fuiste tú, un hombre como yo, mi compañero, y mi amigo familiar.
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 Tomamos juntos una dulce comunión. Caminamos en la casa de Dios con compañía.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 Que la muerte les llegue de repente. Que bajen vivos al Seol. Porque la maldad está entre ellos, en su morada. (Sheol h7585)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
16 En cuanto a mí, invocaré a Dios. Yahvé me salvará.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 Por la tarde, por la mañana y al mediodía, gritaré de angustia. Escuchará mi voz.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 Él ha redimido mi alma en paz de la batalla que había contra mí, aunque hay muchos que se oponen a mí.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 Dios, que está entronizado para siempre, los escuchará y responderá. (Selah) Nunca cambian y no teman a Dios.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 Levanta las manos contra sus amigos. Ha violado su pacto.
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 Su boca era suave como la mantequilla, pero su corazón estaba en guerra. Sus palabras eran más suaves que el aceite, sin embargo, eran espadas desenvainadas.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Echa tu carga sobre Yahvé y él te sostendrá. Él nunca permitirá que los justos sean conmovidos.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 Pero tú, Dios, los harás descender al pozo de la destrucción. Los hombres sanguinarios y engañosos no vivirán ni la mitad de sus días, pero confiaré en ti.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.

< Salmos 55 >