< Salmos 40 >
1 Para el músico principal. Un salmo de David. Esperé pacientemente a Yahvé. Se volvió hacia mí y escuchó mi grito.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
2 También a mí me sacó de un pozo horrible, de la arcilla cenagosa. Puso mis pies en una roca, y me dio un lugar firme para pararme.
Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
3 Ha puesto en mi boca un cántico nuevo, la alabanza a nuestro Dios. Muchos lo verán, y temerán, y confiarán en Yahvé.
Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
4 Dichoso el hombre que hace de Yahvé su confianza, y no respeta a los soberbios, ni a los que se apartan a la mentira.
Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
5 Muchas son, Yahvé, mi Dios, las obras maravillosas que has hecho, y sus pensamientos que son hacia nosotros. No pueden ser declarados de nuevo a usted. Si quisiera declarar y hablar de ellos, son más de los que se pueden contar.
Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
6 Sacrificio y ofrenda que no deseabas. Me has abierto los oídos. No has exigido holocausto ni ofrenda por el pecado.
Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
7 Entonces dije: “He aquí que he venido. Está escrito sobre mí en el libro del pergamino.
Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
8 Me encanta hacer tu voluntad, Dios mío. Sí, tu ley está en mi corazón”.
Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
9 He proclamado la buena noticia de la justicia en la gran asamblea. He aquí que no sellaré mis labios, Yahvé, tú lo sabes.
Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
10 No he ocultado tu justicia en mi corazón. He declarado tu fidelidad y tu salvación. No he ocultado tu amorosa bondad y tu verdad a la gran asamblea.
Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
11 No me niegues tus tiernas misericordias, Yahvé. Que tu amorosa bondad y tu verdad me preserven continuamente.
Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
12 Porque me han rodeado innumerables males. Mis iniquidades me han alcanzado, de modo que no soy capaz de levantar la vista. Son más que los pelos de mi cabeza. Mi corazón me ha fallado.
Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
13 Complácete, Yahvé, en librarme. Apresúrate a ayudarme, Yahvé.
Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
14 Que se decepcionen y se confundan juntos los que buscan mi alma para destruirla. Que retrocedan y sean deshonrados los que se deleitan en mi daño.
Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
15 Que queden desolados por su vergüenza los que me dicen: “¡Ah! ¡Ah!”
Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
16 Que todos los que te buscan se regocijen y se alegren en ti. Que los que aman tu salvación digan continuamente: “¡Sea exaltado Yahvé!”
Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
17 Pero soy pobre y estoy necesitado. Que el Señor piense en mí. Tú eres mi ayuda y mi libertador. No te demores, Dios mío.
Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.