< Salmos 22 >

1 Para el músico principal; ambientado en “La cierva de la mañana”. Un salmo de David. Dios mío, Dios mío, ¿por qué me has abandonado? ¿Por qué estás tan lejos de ayudarme, y de las palabras de mi gemido?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 Dios mío, clamo de día, pero no respondes; en la estación de la noche, y no estoy en silencio.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 Pero tú eres santo, tú que habitas las alabanzas de Israel.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 Nuestros padres confiaron en ti. Confiaron, y tú les entregaste.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 Clamaron a ti y fueron liberados. Confiaron en ti, y no quedaron decepcionados.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 Pero yo soy un gusano y no un hombre; un reproche de los hombres, y despreciado por el pueblo.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 Todos los que me ven se burlan de mí. Me insultan con sus labios. Mueven la cabeza, diciendo,
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 “Confía en Yahvé. Que lo entregue. Que lo rescate, ya que se deleita en él”.
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 Pero tú me sacaste del vientre. Me hiciste confiar en los pechos de mi madre.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 Me arrojaron sobre ti desde el vientre de mi madre. Tú eres mi Dios desde que mi madre me parió.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 No te alejes de mí, porque los problemas están cerca. Porque no hay nadie que ayude.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Muchos toros me han rodeado. Fuertes toros de Basán me han rodeado.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 Abren mucho la boca contra mí, leones desgarrando presas y rugiendo.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 Me derramo como el agua. Todos mis huesos están fuera de lugar. Mi corazón es como la cera. Se derrite dentro de mí.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 Mi fuerza se ha secado como un tiesto. Mi lengua se pega al paladar. Me has llevado al polvo de la muerte.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 Porque los perros me han rodeado. Una compañía de malhechores me ha encerrado. Me han perforado las manos y los pies.
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 Puedo contar todos mis huesos. Me miran y se quedan mirando.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 Se reparten mis vestidos entre ellos. Echaron a suertes mi ropa.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 Pero no te alejes, Yahvé. Tú eres mi ayuda. Apresúrate a ayudarme.
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Libra mi alma de la espada, mi preciosa vida del poder del perro.
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 ¡Sálvame de la boca del león! Sí, me has rescatado de los cuernos de los bueyes salvajes.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 Yo declararé tu nombre a mis hermanos. Entre la asamblea, te alabaré.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Los que temen al Señor, alábenlo. Todos ustedes, descendientes de Jacob, glorifíquenlo. ¡Prepárense ante él, todos los descendientes de Israel!
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Porque no ha despreciado ni abominado la aflicción de los afligidos, tampoco le ha ocultado su rostro; pero cuando le gritó, lo escuchó.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 Mi alabanza a ti viene en la gran asamblea. Pagaré mis votos ante los que le temen.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 Los humildes comerán y se saciarán. Alabarán a Yahvé los que lo buscan. Que vuestros corazones vivan para siempre.
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 Todos los confines de la tierra se acordarán y se volverán a Yahvé. Todos los parientes de las naciones adorarán ante ti.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 Porque el reino es de Yahvé. Él es el gobernante de las naciones.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 Todos los ricos de la tierra comerán y adorarán. Todos los que desciendan al polvo se inclinarán ante él, incluso el que no puede mantener su alma viva.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 La posteridad le servirá. A las generaciones futuras se les hablará del Señor.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 Vendrán y anunciarán su justicia a un pueblo que nacerá, porque lo ha hecho.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.

< Salmos 22 >