< Salmos 2 >

1 Por qué se enfurecen las naciones, ¿y los pueblos traman una cosa vana?
Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
2 Los reyes de la tierra toman posición, y los gobernantes se aconsejan entre sí, contra Yahvé y contra su Ungido, diciendo,
Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
3 “Rompamos sus vínculos, y arrojar sus cuerdas de nosotros”.
Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
4 El que está sentado en los cielos se reirá. El Señor se burlará de ellos.
Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
5 Entonces les hablará en su ira, y aterrorizarlos en su ira:
Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
6 “Pero he puesto a mi Rey en mi santo monte de Sión”.
“Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
7 Voy a contar el decreto: Yahvé me dijo: “Tú eres mi hijo. Hoy me he convertido en tu padre.
Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
8 Pídeme y te daré las naciones como herencia, los confines de la tierra para su posesión.
Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
9 Los romperás con una vara de hierro. Los harás pedazos como una vasija de alfarero”.
Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
10 Ahora, pues, sed sabios, reyes. Instrúyanse, jueces de la tierra.
Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
11 Sirve a Yahvé con temor, y se regocija con el temblor.
Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
12 Dad un homenaje sincero al Hijo, no sea que se enfade y perezcáis en el camino, porque su ira pronto se encenderá. Dichosos los que se refugian en él.
Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.

< Salmos 2 >