< Salmos 147 >

1 Alabado sea Yah, porque es bueno cantar alabanzas a nuestro Dios; porque es agradable y conveniente alabarlo.
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 Yahvé construye Jerusalén. Reúne a los parias de Israel.
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 Él cura a los quebrantados de corazón, y venda sus heridas.
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 Cuenta el número de las estrellas. Los llama a todos por su nombre.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Grande es nuestro Señor, y poderoso en poder. Su comprensión es infinita.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 Yahvé sostiene a los humildes. Derriba a los malvados al suelo.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Canten a Yahvé con acción de gracias. Canta alabanzas con el arpa a nuestro Dios,
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 que cubre el cielo de nubes, que prepara la lluvia para la tierra, que hace crecer la hierba en las montañas.
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 Proporciona alimento para el ganado, y para los jóvenes cuervos cuando llaman.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 No se deleita en la fuerza del caballo. No se complace en las piernas de un hombre.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 Yahvé se complace en los que le temen, en los que esperan en su amorosa bondad.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 ¡Alabado sea Yahvé, Jerusalén! ¡Alabado sea tu Dios, Sión!
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 Porque ha reforzado los barrotes de tus puertas. Él ha bendecido a tus hijos dentro de ti.
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 Él hace la paz en tus fronteras. Te llena de lo mejor del trigo.
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 Él envía su mandamiento a la tierra. Su palabra corre muy rápido.
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 Él da la nieve como la lana, y dispersa la escarcha como las cenizas.
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 Arroja su granizo como si fueran guijarros. ¿Quién puede enfrentarse a su frío?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 Envía su palabra y los derrite. Él hace soplar su viento, y las aguas fluyen.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 Muestra su palabra a Jacob, sus estatutos y sus ordenanzas a Israel.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 No lo ha hecho por cualquier nación. No conocen sus ordenanzas. ¡Alabado sea Yah!
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.

< Salmos 147 >