< Salmos 142 >

1 Una contemplación de David, cuando estaba en la cueva. Una oración. Clamo con mi voz a Yahvé. Con mi voz, pido a Yahvé misericordia.
Maskil ne ta Dawuda. Sa’ad da yake cikin kogo. Addu’a ce. Na yi kuka mai ƙarfi ga Ubangiji; na tā da muryata ga Ubangiji neman jinƙai.
2 Derramo mi queja ante él. Le cuento mis problemas.
Na kawo gunagunina a gabansa; a gabansa na faɗa wahalata.
3 Cuando mi espíritu se sobrecogió dentro de mí, que conocías mi ruta. En el camino en el que camino, han escondido una trampa para mí.
Sa’ad da ƙarfina ya kāre a cikina, kai ne wanda ya san hanyata. A hanyar da nake tafiya mutane sun kafa mini tarko.
4 Mira a mi derecha y ve; porque no hay nadie que se preocupe por mí. El refugio ha huido de mí. Nadie se preocupa por mi alma.
Duba ta damata ka gani; babu wanda ya kula da ni. Ba ni da mafaka; babu wanda ya kula da raina.
5 A ti, Yahvé, te clamé. Le dije: “Tú eres mi refugio, mi parte en la tierra de los vivos”.
Na yi kuka gare ka, ya Ubangiji; Na ce, “Kai ne mafakata, rabona a ƙasar masu rai.”
6 Escucha mi grito, porque estoy desesperado. Líbrame de mis perseguidores, porque son demasiado fuertes para mí.
Ka saurari kukata, gama ina cikin matsananciyar bukata; ka cece ni daga waɗanda suke fafarata, gama sun fi ni ƙarfi sosai.
7 Saca ami alma de la cárcel, para que pueda dar gracias a tu nombre. Los justos me rodearán, porque tú serás bueno conmigo.
Ka’yantar da ni daga kurkuku, don in yabi sunanka. Ta haka masu adalci za su taru kewaye da ni saboda alherinka gare ni.

< Salmos 142 >