< Salmos 122 >

1 Una canción de ascensos. Por David. Me alegré cuando me dijeron, “¡Vamos a la casa de Yahvé!”
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 ¡Nuestros pies están dentro de tus puertas, Jerusalén!
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Jerusalén se construye como una ciudad compacta,
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 donde suben las tribus, incluso las de Yah, según una ordenanza para Israel, para dar gracias al nombre de Yahvé.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 Porque hay tronos establecidos para el juicio, los tronos de la casa de David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Reza por la paz de Jerusalén. Los que te aman prosperarán.
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 Que la paz esté dentro de tus muros, y la prosperidad en sus palacios.
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 Por el bien de mis hermanos y compañeros, Ahora diré: “La paz esté dentro de ti”.
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 Por el bien de la casa de Yahvé nuestro Dios, Buscaré tu bien.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.

< Salmos 122 >