< Salmos 121 >
1 Una canción de ascensos. Alzaré mis ojos a las colinas. ¿De dónde viene mi ayuda?
Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
2 Mi ayuda viene de Yahvé, que hizo el cielo y la tierra.
Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
3 No permitirá que tu pie se mueva. El que te guarda no dormirá.
Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
4 He aquí que el que guarda a Israel no se adormecerá ni dormirá.
tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
5 Yahvé es tu guardián. Yahvé es tu sombra a tu derecha.
Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
6 El sol no te dañará de día, ni la luna de noche.
rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
7 El Señor te guardará de todo mal. Él guardará tu alma.
Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
8 Yahvé guardará tu salida y tu entrada, a partir de este momento, y para siempre.
Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.