< Salmos 106 >

1 ¡Alabado sea Yahvé! Dad gracias a Yahvé, porque es bueno, porque su bondad es eterna.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 ¿Quién puede pronunciar los actos poderosos de Yahvé? o declarar plenamente todas sus alabanzas?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Dichosos los que guardan la justicia. Dichoso el que hace lo correcto en todo momento.
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Acuérdate de mí, Yahvé, con el favor que muestras a tu pueblo. Visítame con tu salvación,
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 para que vea la prosperidad de tus elegidos, para que me regocije en la alegría de tu nación, para que me gloríe con tu herencia.
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Hemos pecado con nuestros padres. Hemos cometido una iniquidad. Hemos hecho maldades.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Nuestros padres no entendieron tus maravillas en Egipto. No recordaron la multitud de tus bondades amorosas, pero fueron rebeldes en el mar, incluso en el Mar Rojo.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Sin embargo, los salvó por su nombre, para dar a conocer su poderoso poder.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 También reprendió al Mar Rojo, y se secó; por lo que los condujo a través de las profundidades, como a través de un desierto.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 Los salvó de la mano del que los odiaba, y los redujo de la mano del enemigo.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 Las aguas cubrieron a sus adversarios. No quedaba ni uno de ellos.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Entonces creyeron en sus palabras. Cantaron sus alabanzas.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Pronto olvidaron sus obras. No esperaron su consejo,
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 pero cedió al deseo en el desierto, y puso a prueba a Dios en el páramo.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 Les concedió su petición, sino que enviaron a su alma la delgadez.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 También envidiaban a Moisés en el campamento, y Aarón, el santo de Yahvé.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 La tierra se abrió y se tragó a Datán, y cubrió la compañía de Abiram.
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 Se encendió un fuego en su compañía. La llama quemó a los malvados.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 Hicieron un becerro en Horeb, y adoraron una imagen fundida.
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 Así intercambiaron su gloria para una imagen de un toro que come hierba.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 Se olvidaron de Dios, su Salvador, que había hecho grandes cosas en Egipto,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 obras maravillosas en la tierra de Cam, y cosas impresionantes junto al Mar Rojo.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 Por eso dijo que los destruiría, si Moisés, su elegido, no se hubiera puesto delante de él en la brecha, para alejar su ira, para que no los destruya.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Sí, despreciaron la tierra agradable. No creyeron en su palabra,
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 sino que murmuraban en sus tiendas, y no escucharon la voz de Yahvé.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Por eso les juró que los derrocaría en el desierto,
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 que él derrocaría a su descendencia entre las naciones, y dispersarlos en las tierras.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 También se unieron a Baal Peor, y comieron los sacrificios de los muertos.
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 Así le provocaron la ira con sus actos. La peste se abatió sobre ellos.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Entonces Finees se levantó y ejecutó el juicio, por lo que la plaga fue detenida.
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 Eso se le acreditó como justicia, para todas las generaciones venideras.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 También lo enfurecieron en las aguas de Meribá, por lo que Moisés se preocupó por ellos;
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 porque eran rebeldes a su espíritu, habló precipitadamente con los labios.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 No destruyeron los pueblos, como les ordenó Yahvé,
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 sino que se mezclaron con las naciones, y aprendieron sus obras.
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 Servían a sus ídolos, que se convirtió en una trampa para ellos.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 Sí, sacrificaron a sus hijos e hijas a los demonios.
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 Derramaron sangre inocente, incluso la sangre de sus hijos y de sus hijas, que sacrificaron a los ídolos de Canaán. La tierra estaba contaminada con sangre.
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 Así se contaminaron con sus obras, y se prostituyeron en sus actos.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Por eso Yahvé ardió de ira contra su pueblo. Aborrecía su herencia.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 Los entregó en manos de las naciones. Los que los odiaban los gobernaban.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Sus enemigos también los oprimieron. Fueron sometidos bajo su mano.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Los rescató muchas veces, pero fueron rebeldes en su consejo, y fueron abatidos en su iniquidad.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Sin embargo, él consideró su angustia, cuando escuchó su grito.
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 Se acordó por ellos de su pacto, y se arrepintió según la multitud de sus bondades.
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 También hizo que se compadecieran de ellos por todos aquellos que los llevaron cautivos.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Sálvanos, Yahvé, nuestro Dios, reunirnos de entre las naciones, para dar gracias a tu santo nombre, ¡para triunfar en tu alabanza!
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Bendito sea Yahvé, el Dios de Israel, ¡desde la eternidad hasta la eternidad! Que todo el pueblo diga: “Amén”. ¡Alabado sea Yah!
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.

< Salmos 106 >