< Salmos 103 >

1 Por David. ¡Alabado sea Yahvé, alma mía! Todo lo que hay dentro de mí, alaba su santo nombre.
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
2 Alaba a Yahvé, alma mía, y no olvides todos sus beneficios,
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
3 que perdona todos tus pecados, que cura todas tus enfermedades,
wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
4 que redime tu vida de la destrucción, que te corona de bondad y misericordia,
wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
5 que satisface tu deseo con cosas buenas, para que tu juventud se renueve como la del águila.
Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
6 Yahvé ejecuta actos justos, y justicia para todos los oprimidos.
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7 Dio a conocer sus caminos a Moisés, sus hechos a los hijos de Israel.
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8 El Señor es misericordioso y bondadoso, lento para la ira, y abundante en bondad amorosa.
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9 No siempre acusará; tampoco se quedará enfadado para siempre.
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10 No nos ha tratado según nuestros pecados, ni nos ha pagado nuestras iniquidades.
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11 Porque como los cielos son altos sobre la tierra, tan grande es su bondad para con los que le temen.
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12 Tan lejos como el este está del oeste, hasta ahora ha quitado de nosotros nuestras transgresiones.
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13 Como un padre se compadece de sus hijos, por lo que Yahvé se compadece de los que le temen.
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
14 Porque él sabe cómo estamos hechos. Recuerda que somos polvo.
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
15 En cuanto al hombre, sus días son como la hierba. Como una flor del campo, así florece.
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
16 Porque el viento pasa por encima, y se va. Su lugar ya no lo recuerda.
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
17 Pero la bondad de Yahvé es eterna con los que le temen, su justicia a los hijos de los hijos,
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
18 a los que guardan su pacto, a los que se acuerdan de obedecer sus preceptos.
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
19 Yahvé ha establecido su trono en los cielos. Su reino gobierna sobre todo.
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
20 Alabad a Yahvé, ángeles suyos, que son poderosos en fuerza, que cumplen su palabra, obedeciendo la voz de su palabra.
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
21 Alabad a Yahvé, todos sus ejércitos, vosotros, siervos suyos, que hacéis su voluntad.
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
22 Alabad a Yahvé, todas sus obras, en todos los lugares de su dominio. ¡Alabado sea Yahvé, mi alma!
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.

< Salmos 103 >