< Salmos 102 >

1 Oración del afligido, cuando está agobiado y vierte su queja ante Yahvé. ¡Escucha mi oración, Yahvé! Deja que mi grito llegue a ti.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 No escondas tu rostro de mí en el día de mi angustia. Poner el oído en mí. Contéstame rápidamente en el día cuando llame.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Porque mis días se consumen como el humo. Mis huesos están quemados como una antorcha.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Mi corazón se ha marchitado como la hierba, y se ha secado, porque me olvido de comer mi pan.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Por la voz de mi gemido, mis huesos se pegan a mi piel.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Soy como un pelícano del desierto. Me he vuelto como un búho de los lugares de desecho.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 Yo vigilo, y me he vuelto como un gorrión que está solo en el tejado.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Mis enemigos me reprochan todo el día. Los que están enfadados conmigo utilizan mi nombre como una maldición.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 Porque he comido cenizas como pan, y mezclé mi bebida con lágrimas,
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 a causa de tu indignación y tu ira; porque me has cogido y me has tirado.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Mis días son como una larga sombra. Me he marchitado como la hierba.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 Pero tú, Yahvé, permanecerás para siempre; tu fama perdura por todas las generaciones.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Te levantarás y tendrás piedad de Sión, pues es hora de apiadarse de ella. Sí, ha llegado el momento de la puesta en escena.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Porque tus siervos se complacen en sus piedras, y apiádate de su polvo.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Así las naciones temerán el nombre de Yahvé, todos los reyes de la tierra tu gloria.
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 Porque Yahvé ha edificado a Sión. Ha aparecido en su gloria.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 Ha respondido a la oración de los indigentes, y no ha despreciado su oración.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Esto se escribirá para la generación venidera. Un pueblo que será creado alabará a Yah,
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 porque ha mirado desde la altura de su santuario. Desde el cielo, Yahvé vio la tierra,
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 para escuchar los gemidos del prisionero, para liberar a los condenados a muerte,
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 para que los hombres anuncien el nombre de Yahvé en Sión, y su alabanza en Jerusalén,
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 cuando los pueblos están reunidos, los reinos, para servir a Yahvé.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 Él debilitó mis fuerzas a lo largo del recorrido. Acortó mis días.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Dije: “Dios mío, no me lleves a la mitad de mis días. Sus años son a través de todas las generaciones.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Desde antaño, tú pusiste los cimientos de la tierra. Los cielos son obra de tus manos.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Ellos perecerán, pero tú perdurarás. Sí, todos ellos se desgastarán como una prenda de vestir. Los cambiarás como un manto, y serán cambiados.
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 Pero tú eres el mismo. Tus años no tendrán fin.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Los hijos de tus siervos continuarán. Su descendencia se establecerá ante ti”.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< Salmos 102 >