< Salmos 10 >

1 ¿Por qué te mantienes alejado, Yahvé? ¿Por qué te escondes en los momentos difíciles?
Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa? Me ya sa kake ɓoye kanka a lokutan wahala?
2 En la arrogancia, los malvados persiguen a los débiles. Quedan atrapados en los esquemas que idean.
Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi, waɗanda yake kama cikin makircin da ya shirya.
3 Porque el malvado se jacta de los antojos de su corazón. Bendice a los codiciosos y condena a Yahvé.
Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa; yana albarkaci mai haɗama yana kuma ƙin Ubangiji.
4 El malvado, en la soberbia de su rostro, no tiene espacio en sus pensamientos para Dios.
Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah; cikin tunaninsa ba ya ba da wata dama saboda Allah.
5 Sus caminos son prósperos en todo momento. Es arrogante, y tus leyes están lejos de su vista. En cuanto a todos sus adversarios, se burla de ellos.
Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara; yana da girman kai kuma dokokinka suna nesa da shi; yakan yi wa dukan abokan gābansa duban reni.
6 Dice en su corazón: “No seré sacudido. Por generaciones no tendré problemas”.
Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni; kullum zan yi murna ba zan taɓa shiga wahala ba.”
7 Su boca está llena de maldiciones, engaños y opresión. Bajo su lengua hay maldad e iniquidad.
Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.
8 Está al acecho cerca de las aldeas. Desde las emboscadas, asesina a los inocentes. Sus ojos están secretamente puestos en los indefensos.
Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka; daga kwanton yakan kashe marar laifi. Yana kallon waɗanda za su shiga hannunsa a ɓoye.
9 Acecha en secreto como un león en su emboscada. Está al acecho para atrapar a los indefensos. Atrapa al indefenso cuando lo atrae en su red.
Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki. Yakan yi kwanto don yă kama marasa ƙarfi; yakan kama marasa ƙarfi yă ja su cikin ragarsa.
10 Los indefensos son aplastados. Se derrumban. Caen bajo su fuerza.
Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi; sukan fāɗi a ƙarƙashin ƙarfinsa.
11 Dice en su corazón: “Dios se ha olvidado. Oculta su rostro. Nunca lo verá”.
Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta; ya rufe fuskarsa ba ya gani.”
12 ¡Levántate, Yahvé! ¡Dios, levanta tu mano! No te olvides de los indefensos.
Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah. Kada ka manta da marasa ƙarfi.
13 Por qué el malvado condena a Dios, y decir en su corazón: “¿Dios no me pedirá cuentas?”
Don me mugun mutum zai ƙi Allah? Don me yakan ce wa kansa, “Allah ba zai nemi hakki daga gare ni ba”?
14 Pero tú ves problemas y penas. Lo consideras para tomarlo en tu mano. Ayudas a la víctima y a los huérfanos.
Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki; kana lura da yadda suke ɗaukansu a hannu. Marar taimako kan danƙa kansa gare ka; kai ne mai taimakon marayu
15 Rompe el brazo de los malvados. En cuanto al hombre malo, busca su maldad hasta que no la encuentres.
Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum; ka nemi hakki daga gare shi saboda muguntar da ba za a gane ba.
16 ¡Yahvé es Rey por los siglos de los siglos! Las naciones perecerán fuera de su tierra.
Ubangiji Sarkin har abada abadin ne; al’ummai za su hallaka daga ƙasarsa.
17 Yahvé, tú has escuchado el deseo de los humildes. Prepararás su corazón. Harás que tu oído escuche,
Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,
18 para juzgar a los huérfanos y a los oprimidos, para que el hombre que es de la tierra no aterrorice más.
kana kāre marayu da waɗanda aka danne, domin mutum, wanda yake na duniya kada ƙara haddasa wata razana.

< Salmos 10 >