< Proverbios 2 >
1 Hijo mío, si recibes mis palabras, y guardad mis mandamientos en vuestro interior,
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 para que vuelvas tu oído a la sabiduría, y aplica tu corazón a la comprensión;
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 sí, si se llama al discernimiento, y levanta tu voz para que te entiendan;
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 si la buscas como plata, y buscarla como a los tesoros escondidos;
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 entonces entenderás el temor de Yahvé, y encontrar el conocimiento de Dios.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 Porque Yahvé da sabiduría. De su boca sale el conocimiento y la comprensión.
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 Él acumula la sana sabiduría para los rectos. Es un escudo para los que caminan con integridad,
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 para que guarde los caminos de la justicia, y preservar el camino de sus santos.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Entonces entenderás la rectitud y la justicia, la equidad y todo buen camino.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 Porque la sabiduría entrará en tu corazón. El conocimiento será agradable para tu alma.
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 La discreción velará por ti. La comprensión te mantendrá,
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 para librarte del camino del mal, de los hombres que hablan cosas perversas,
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 que abandonan los caminos de la rectitud, para andar por los caminos de la oscuridad,
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 que se alegran de hacer el mal, y se deleitan en la perversidad del mal,
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 que son torcidos en sus caminos, y descarriados en sus caminos,
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 para librarte de la mujer extraña, incluso de la extranjera que halaga con sus palabras,
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 que abandona al amigo de su juventud, y olvida el pacto de su Dios;
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 por su casa lleva a la muerte, sus caminos a los espíritus difuntos.
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 Ninguno de los que van a ella regresa, ni alcanzan los caminos de la vida.
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 Por lo tanto, camina por el camino de los hombres buenos, y guarda los caminos de los justos.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 Porque los rectos habitarán la tierra. Lo perfecto permanecerá en él.
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 Pero los malvados serán eliminados de la tierra. Los traidores serán desarraigados de ella.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.