< Miqueas 1 >

1 Palabra de Yahvé que vino a Miqueas de Morashet en los días de Jotam, Acaz y Ezequías, reyes de Judá, que vio sobre Samaria y Jerusalén.
Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
2 ¡Oíd, pueblos, todos vosotros! Escucha, oh tierra, y todo lo que hay en ella. Que el Señor Yahvé sea testigo contra ti, al Señor de su santo templo.
Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.
3 Porque he aquí que Yahvé sale de su lugar, y bajará y pisará los lugares altos de la tierra.
Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa; zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.
4 Las montañas se derriten bajo él, y los valles se deshacen como la cera ante el fuego, como las aguas que se vierten por un lugar escarpado.
Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa, kamar kaki a gaban wuta, kwaruruka kuma za su ɓace, kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.
5 “Todo esto es por la desobediencia de Jacob, y por los pecados de la casa de Israel. ¿Cuál es la desobediencia de Jacob? ¿No es Samaria? ¿Y cuáles son los lugares altos de Judá? ¿No son Jerusalén?
Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub, da kuma zunuban gidan Isra’ila ne. Mene ne laifin Yaƙub? Shin, ba Samariya ba ce? Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda? Shin, ba Urushalima ba ce?
6 Por eso haré que Samaria sea como un montón de escombros del campo, como lugares para plantar viñedos; y derramaré sus piedras en el valle, y yo descubriré sus cimientos.
“Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji, wurin noman inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari in kuma bar harsashin gininta a bayyane.
7 Todos sus ídolos serán despedazados, todos sus regalos del templo serán quemados con fuego, y destruiré todas sus imágenes; pues del alquiler de una prostituta los ha reunido, y al alquiler de una prostituta volverán”.
Za a ragargaje dukan allolinta; za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta; zan lalatar da dukan gumakanta. Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su, ga karuwanci kuma za su koma.”
8 Por esto me lamentaré y lloraré. Iré despojado y desnudo. Aullaré como los chacales y llorar como los avestruces.
Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka; zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara. Zan yi kuka kamar dila, in yi baƙin ciki kamar mujiya.
9 Porque sus heridas son incurables; porque ha llegado incluso a Judá. Llega hasta la puerta de mi pueblo, incluso a Jerusalén.
Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne; ya bazu har Yahuda. Ya ma kai bakin ƙofar mutanena, har ma Urushalima da kanta.
10 No lo cuentes en Gat. No llores en absoluto. En Beth Ophrah me he revolcado en el polvo.
Kada a faɗe shi a Gat; kada ma a yi kuka. A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙura a Bet-Leyafra.
11 Pasa, habitante de Shaphir, en desnudez y vergüenza. El habitante de Zaanan no saldrá. El lamento de Beth Ezel te quitará su protección.
Ku wuce tsirara da kuma kunya, ku mazaunan Shafir. Bet-Ezel tana makoki domin babu wani daga Za’anan da ya fito don yă taimaka.
12 Porque el habitante de Maroth espera ansiosamente el bien, porque el mal ha bajado de Yahvé a la puerta de Jerusalén.
Mazaunan Marot sun ƙosa su ga alheri, amma Ubangiji ya sauko da azaba, har zuwa ƙofar Urushalima.
13 Engancha el carro al veloz corcel, habitante de Laquis. Fue el principio del pecado para la hija de Sión; porque las transgresiones de Israel fueron encontradas en ti.
Ku da kuke zama a Lakish, ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi. Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, gama an sami laifofin Isra’ila a cikinku.
14 Por lo tanto, darás un regalo de despedida a Moresheth Gath. Las casas de Achzib serán un engaño para los reyes de Israel.
Saboda haka za ku ba da kyautan bankwana ga Moreshet Gat. Garin Akzib zai zama abin yaudara ga sarakunan Isra’ila.
15 Aún traeré un conquistador a ustedes, habitantes de Mareshah. La gloria de Israel llegará a Adulam.
Ku mazaunan Maresha Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi. Sarakunan Isra’ila za su gudu zuwa Adullam.
16 Aféitate la cabeza, y cortarte el pelo por los hijos de tu deleite. Agranda tu calvicie como el buitre, ¡porque han ido al cautiverio de ti!
Ku aske kanku ƙwal don makoki, ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu. Gama za a ja’ya’yan da kuke farin ciki a kai su bauta.

< Miqueas 1 >