< Levítico 6 >

1 Yahvé habló a Moisés, diciendo:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Si alguno peca y comete una transgresión contra Yahvé, y trata con falsedad a su prójimo en un asunto de depósito, o de negociación, o de robo, o ha oprimido a su prójimo,
“In wani ya yi zunubi bai kuma yi aminci ga Ubangiji ba, wato, ta wurin yin wa abokin zamansa karya game da ajiyar da abokin ya ba shi amana, ko a kan wani alkawarin da suka yi wa juna, ko kuwa a kan yă cuci abokin,
3 o ha encontrado lo que se había perdido y ha mentido sobre ello, y jurando en una mentira-en cualquiera de estas cosas que un hombre peca en sus acciones—
ko kuma idan ya sami abin da ya ɓace amma ya yi ƙarya cewa bai samu ba. Ko ya yi rantsuwar ƙarya a kan duk irin abubuwan da akan aikata na laifi,
4 entonces será, si ha pecado, y es culpable, deberá restaurar lo que tomó por robo, o la cosa que ha obtenido por opresión, o el depósito que le fue encomendado, o la cosa perdida que encontró,
sa’ad da mutum ya yi irin laifin nan, ya kuwa tabbata mai laifi ne, to, sai yă komar da abin da ya ƙwace, ko abin da ya samu ta hanyar zalunci, ko abin da aka ba shi ajiya, ko abin da ya tsinta.
5 o cualquier cosa sobre la que ha jurado en falso: lo restituirá íntegramente, y le añadirá una quinta parte más. Lo devolverá a su dueño el día que sea declarado culpable.
Zai mai da abin da ya yi rantsuwar ƙarya a kai. Zai mayar wa mai abin da abinsa a yadda yake, har yă ƙara kashi ashirin bisa ɗari na abin. A ranar da zai yi hadaya don laifinsa, a ranar ce zai mayar wa mai abin da abinsa.
6 Traerá su ofrenda por la culpa a Yahvé: un carnero sin defecto del rebaño, según tu estimación, como ofrenda por la culpa, al sacerdote.
A matsayin hakki kuwa, dole yă kawo wa firist, wato, ga Ubangiji, hadaya rago marar lahani kuma wanda aka kimanta tamaninsa daga garke don laifinsa.
7 El sacerdote hará expiación por él ante Yahvé, y se le perdonará todo lo que haga para ser culpable.”
Ta haka firist zai yi kafara dominsa a gaban Ubangiji, za a kuwa gafarta masa irin laifin da ya yi.”
8 Yahvé habló a Moisés, diciendo:
Ubangiji ya ce wa Musa,
9 “Manda a Aarón y a sus hijos, diciendo: ‘Esta es la ley del holocausto: el holocausto estará sobre el hogar del altar toda la noche hasta la mañana; y el fuego del altar se mantendrá encendido sobre él.
“Ka ba Haruna da’ya’yansa maza wannan umarni, ‘Waɗannan su ne ƙa’idodi don hadaya ta ƙonawa. Hadaya ta ƙonawa za tă kasance a bagade dukan dare, sai da safe, kuma dole a bar wutar tă yi ta ci a bisa bagaden.
10 El sacerdote se pondrá su vestimenta de lino, y se pondrá sus pantalones de lino sobre su cuerpo; y quitará las cenizas de donde el fuego haya consumido el holocausto en el altar, y las pondrá junto al altar.
Sa’an nan firist zai sa rigunarsa ta lilin da kuma rigar lilin da ake sa a ciki, sa’an nan yă kwashe tokan hadaya ta ƙonawa da wuta da ta ci a kan bagaden, yă sa kusa da bagaden.
11 Se quitará sus vestidos y se pondrá otros, y llevará las cenizas fuera del campamento a un lugar limpio.
Sa’an nan yă tuɓe waɗannan rigunan yă sa waɗansu, sa’an nan yă ɗauki tokar yă kai waje da sansani zuwa inda yake da tsabta.
12 El fuego del altar se mantendrá encendido en él, no se apagará; y el sacerdote quemará leña en él cada mañana. Pondrá el holocausto en orden sobre él, y quemará sobre él la grasa de los sacrificios de paz.
Dole a bar wutar da take bisa bagaden tă yi ta ci; kada tă mutu. Kowace safiya firist zai ƙara itacen wuta, yă shirya hadaya ta ƙonawa a bisa wutar yă kuma ƙone kitsen hadaya ta salama a kansa.
13 El fuego se mantendrá encendido sobre el altar continuamente; no se apagará.
Dole a bar wutar tă ci gaba da ci a bisa bagade; kada tă mutu.
14 “‘Esta es la ley de la ofrenda de cereal: los hijos de Aarón la ofrecerán ante Yahvé, delante del altar.
“‘Waɗannan su ne ƙa’idodi domin hadaya ta gari.’Ya’yan Haruna za su kawo ta a gaban Ubangiji, a gaban bagaden.
15 El hijo de Aarón tomará de allí un puñado de la flor de harina de la ofrenda, y de su aceite, y todo el incienso que esté sobre la ofrenda, y lo hará arder sobre el altar en olor agradable, como su porción conmemorativa, para Yahvé.
Firist zai ɗiba garin hadayar mai laushin wanda aka zuba masa mai da kuma turare cike da tafin hannu. Zai ƙona wannan a bisa bagaden, hadaya ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji don tunawa.
16 Lo que quede de ella lo comerán Aarón y sus hijos. Se comerá sin levadura en un lugar sagrado. Lo comerán en el atrio de la Tienda de Reunión.
Haruna da’ya’yansa maza za su ci sauran, amma za a ci shi ba tare da yisti ba a tsattsarkan wuri; za su ci shi a harabar Tentin Sujada.
17 No se cocinará con levadura. Yo se lo he dado como su porción de mis ofrendas hechas por el fuego. Es muy sagrada, al igual que la ofrenda por el pecado y la ofrenda por la culpa.
Ba za a toya shi da yisti ba; na ba su yă zama rabonsu daga cikin hadayun da ake ƙonawa da wuta, abu ne mafi tsarki, kamar hadaya don zunubi da laifi.
18 Todo varón de los hijos de Aarón comerán de ella, como su porción para siempre a lo largo de vuestras generaciones, de las ofrendas quemadas de Yahvé. El que las toque será santo”.
Kowane ɗa namiji cikin zuriyar Haruna zai iya cinsa. Wannan rabonsa ne na kullum na hadayar da aka yi ga Ubangiji da wuta. Wannan madawwamiyar doka ce cikin zamananku duka. Duk abin da ya taɓa hadayun zai tsarkaka.’”
19 Yahvé habló a Moisés diciendo:
Ubangiji ya kuma ce wa Musa,
20 “Esta es la ofrenda de Aarón y de sus hijos, que ofrecerán a Yahvé el día en que sea ungido: la décima parte de un efa de harina fina como ofrenda perpetua, la mitad por la mañana y la otra mitad por la tarde.
“Wannan ne hadayar da Haruna da’ya’yansa maza za su kawo ga Ubangiji a ranar da za a naɗa su firistoci, humushin garwan gari mai laushi a matsayin hadaya ta gari na kullum, rabinsa da safe, rabinsa kuma da yamma.
21 Se hará con aceite en una plancha. Cuando esté empapado, lo traerás. Ofrecerás la ofrenda de comida en trozos cocidos como aroma agradable a Yahvé.
A shirya shi da mai a kwanon tuya, a kawo shi kwaɓaɓɓe sosai, a miƙa shi hadaya ta gari dunƙule-dunƙule don ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
22 La ofrecerá el sacerdote ungido que estará en su lugar de entre sus hijos. Como estatuto para siempre, será quemada en su totalidad a Yahvé.
Duk wanda aka naɗa daga’ya’yan Haruna yă zama firist a madadinsa, shi ne zai miƙa wannan hadayar ga Ubangiji. Zai ƙone hadayar ƙurmus. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce har abada.
23 Toda ofrenda de un sacerdote será quemada por completo. No se comerá”.
Kowace hadaya ta gari ta firist, za a ƙone ta ƙurmus, ba za a ci ba.”
24 Yahvé habló a Moisés, diciendo:
Ubangiji ya ce wa Musa,
25 “Habla a Aarón y a sus hijos, diciendo: ‘Esta es la ley del sacrificio por el pecado: en el lugar donde se mata el holocausto, se matará el sacrificio por el pecado delante de Yahvé. Es algo muy sagrado.
“Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, ‘Waɗannan su ne ƙa’idodi domin hadaya don zunubi. Za a yanka hadaya don zunubi a gaban Ubangiji a inda ake yankan hadaya ta ƙonawa; dole tă kasance mai tsarki.
26 El sacerdote que la ofrezca por el pecado la comerá. Se comerá en un lugar sagrado, en el atrio de la Tienda de Reunión.
Firist da ya miƙa ta zai ci, za a ci ta a tsattsarkan wuri, a harabar Tentin Sujada.
27 Todo lo que toque su carne será sagrado. Cuando su sangre haya sido rociada sobre una prenda de vestir, lavarás la prenda sobre la que fue rociada en un lugar santo.
Duk abin da ya taɓa wani sashe na naman, zai zama da tsarki, kuma in wani jini ya ɗiga a riga, dole ka wanke shi a tsattsarkan wuri.
28 Pero la vasija de barro en que se haya cocido se romperá; y si se ha cocido en una vasija de bronce, se lavará y se enjuagará con agua.
Dole a farfashe tukunyar lakar da aka dafa naman a ciki; amma in an dafa a tukunyar tagulla, sai a kankare tukunyar, a kuma ɗauraye da ruwa.
29 Todo varón de entre los sacerdotes comerá de ella. Es algo muy sagrado.
Kowane namiji a iyalin firistoci zai iya ci; gama abu ne mafi tsarki.
30 No se comerá ninguna ofrenda por el pecado cuya sangre se introduzca en la Tienda de Reunión para hacer expiación en el Lugar Santo. Se quemará con fuego.
Amma duk wata hadaya don zunubi wadda aka kawo jininta cikin Tentin Sujada don a yi kafara a Wuri Mai Tsarki, ba za a ci ba. A maimako haka za a ƙone ta ɗungum.

< Levítico 6 >