< Josué 15 >
1 La suerte de la tribu de los hijos de Judá, según sus familias, fue hasta el límite de Edom, hasta el desierto de Zin hacia el sur, en el extremo del sur.
An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
2 Su límite sur era desde el extremo del Mar Salado, desde la bahía que mira hacia el sur;
Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
3 y salía hacia el sur de la subida de Akrabbim, y pasaba por Zin, y subía por el sur de Cades Barnea, y pasaba por Esrom, subía por Addar, y se volvía hacia Karka;
zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
4 y pasaba por Azmón, salía por el arroyo de Egipto; y el límite terminaba en el mar. Esta será su frontera sur.
Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
5 El límite oriental era el Mar Salado, hasta el final del Jordán. El límite del norte era desde la bahía del mar hasta el final del Jordán.
Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
6 El límite subía hasta Bet Hogá, y pasaba por el norte de Bet Araba; y el límite subía hasta la piedra de Bohán, hijo de Rubén.
wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
7 La frontera subía hasta Debir desde el valle de Acor, y así hacia el norte, mirando hacia Gilgal, que está frente a la subida de Adummim, que está al lado sur del río. La frontera pasaba hasta las aguas de En Shemesh, y terminaba en En Rogel.
Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
8 La frontera subía por el valle del hijo de Hinom hasta el lado del jebuseo (también llamado Jerusalén) hacia el sur; y la frontera subía hasta la cima del monte que está frente al valle de Hinom hacia el oeste, que está en la parte más lejana del valle de Refaim hacia el norte.
Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
9 La frontera se extendía desde la cima del monte hasta el manantial de las aguas de Neftoa, y salía a las ciudades del monte Efrón; y la frontera se extendía hasta Baalá (también llamada Quiriat Jearim);
Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
10 y la frontera giraba desde Baalá hacia el oeste, hacia el monte Seir, y pasaba al lado del monte Jearim (también llamado Cesalón), al norte, y bajaba a Bet Semes, y pasaba junto a Timná;
Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
11 y la frontera salía al lado de Ecrón hacia el norte; y la frontera se extendía hasta Siquerón, y pasaba por el monte Baalá, y salía por Jabneel; y las salidas de la frontera estaban en el mar.
Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
12 El límite occidental llegaba hasta la orilla del gran mar. Esta es la frontera de los hijos de Judá según sus familias.
Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
13 Le dio a Caleb, hijo de Jefone, una porción entre los hijos de Judá, según el mandato de Yahvé a Josué, hasta Quiriat Arba, llamada así por el padre de Anac (también llamada Hebrón).
Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
14 Caleb expulsó a los tres hijos de Anac Sesai, Ahiman y Talmai, hijos de Anac.
Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
15 Subió contra los habitantes de Debir, que antes se llamaba Kiriath Sepher.
Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
16 Caleb dijo: “Al que ataque a Quiriat-Sfer y lo tome, le daré a mi hija Acsa como esposa”.
Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
17 La tomó Othniel, hijo de Kenaz, hermano de Caleb, y le dio a Acsa, su hija, como esposa.
Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
18 Cuando ella llegó, le hizo pedir a su padre un campo. Ella se bajó del asno, y Caleb le dijo: “¿Qué quieres?”
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
19 Ella dijo: “Dame una bendición. Ya que me has puesto en la tierra del Sur, dame también manantiales de agua”. Así que le dio los muelles superiores y los inferiores.
Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
20 Esta es la herencia de la tribu de los hijos de Judá según sus familias.
Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
21 Las ciudades más lejanas de la tribu de los hijos de Judá hacia la frontera de Edom, en el sur, fueron Kabzeel, Eder, Jagur,
Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
22 Kinah, Dimonah, Adadah,
Kina, Dimona, Adada,
23 Kedesh, Hazor, Ithnan,
Kedesh, Hazor, Itnan,
25 Hazor Hadattah, Kerioth Hezron (también llamada Hazor),
Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
27 Hazar Gaddah, Heshmon, Beth Pelet,
Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
28 Hazar Shual, Beersheba, Biziothiah,
Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
30 Eltolad, Chesil, Hormah,
Eltolad, Kesil, Horma,
31 Ziklag, Madmannah, Sansannah,
Ziklag, Madmanna, Sansanna,
32 Lebaoth, Shilhim, Ain y Rimmon. Todas las ciudades son veintinueve, con sus aldeas.
Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
33 En la tierra baja, Eshtaol, Zorah, Ashnah,
Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
34 Zanoah, En Gannim, Tappuah, Enam,
Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
35 Jarmuth, Adullam, Socoh, Azekah,
Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
36 Shaaraim, Adithaim y Gederah (o Gederothaim); catorce ciudades con sus aldeas.
Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
37 Zenan, Hadashah, Migdal Gad,
Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
38 Dilean, Mizpa, Joktheel,
Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
39 Lachish, Bozkath, Eglon,
Lakish, Bozkat, Eglon,
40 Cabbon, Lahmam, Chitlish,
Kabbon, Lahman, Kitlish,
41 Gederoth, Beth Dagon, Naamah, y Makkedah; dieciséis ciudades con sus aldeas.
Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
44 Keilá, Achzib y Maresá; nueve ciudades con sus aldeas.
Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
45 Ecrón, con sus ciudades y sus aldeas;
Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
46 desde Ecrón hasta el mar, todos los que estaban junto a Asdod, con sus aldeas.
yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
47 Asdod, sus ciudades y sus aldeas; Gaza, sus ciudades y sus aldeas; hasta el arroyo de Egipto, y el gran mar con su costa.
Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
48 En la región de las colinas, Shamir, Jattir, Socoh,
Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
49 Dannah, Kiriath Sannah (que es Debir),
Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
51 Goshen, Holon y Giloh; once ciudades con sus aldeas.
Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
53 Janim, Beth Tappuah, Aphekah,
Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
54 Humtah, Kiriath Arba (también llamada Hebrón) y Zior; nueve ciudades con sus aldeas.
Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
55 Maón, Carmelo, Zif, Jutah,
Mawon, Karmel, Zif, Yutta
56 Jezreel, Jocdeam, Zanoa,
Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
57 Caín, Guibeá y Timná; diez ciudades con sus aldeas.
Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
58 Halhul, Beth Zur, Gedor,
Halhul, Bet-Zur, Gedor,
59 Maarath, Beth Anoth y Eltekon; seis ciudades con sus aldeas.
Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
60 Kiriath Baal (también llamada Kiriath Jearim), y Rabbah; dos ciudades con sus aldeas.
Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
61 En el desierto, Bet Araba, Middin, Secacah,
Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
62 Nibshan, la Ciudad de la Sal y En Gedi; seis ciudades con sus aldeas.
Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
63 En cuanto a los jebuseos, habitantes de Jerusalén, los hijos de Judá no pudieron expulsarlos; pero los jebuseos viven con los hijos de Judá en Jerusalén hasta el día de hoy.
Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.