< Josué 13 >

1 Josué era ya viejo y de edad avanzada. Yahvé le dijo: “Eres viejo y avanzado en años, y aún queda mucha tierra por poseer.
Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
2 “Esta es la tierra que aún queda todas las regiones de los filisteos, y todos los guesuritas;
“Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
3 desde el Shihor, que está delante de Egipto, hasta la frontera de Ecrón hacia el norte, que se cuenta como cananea; los cinco señores de los filisteos: los gazitas, los asdoditas, los ascalonitas, los gittitas y los ecronitas; también los avvim,
Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
4 al sur; toda la tierra de los cananeos, y Meará que pertenece a los sidonios, hasta Afec, hasta la frontera de los amorreos;
Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
5 y la tierra de los gebalitas, y todo el Líbano, hacia la salida del sol, desde Baal Gad bajo el monte Hermón hasta la entrada de Hamat;
da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
6 todos los habitantes de la región montañosa desde el Líbano hasta Misrefot Maim, todos los sidonios. Los expulsaré de delante de los hijos de Israel. Sólo asigna a Israel como herencia, como te he ordenado.
“Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
7 Ahora, pues, reparte esta tierra en herencia a las nueve tribus y a la media tribu de Manasés.”
ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
8 Con él, los rubenitas y los gaditas recibieron la herencia que les dio Moisés, al otro lado del Jordán, hacia el este, tal como se la dio Moisés, siervo de Yahvé:
Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
9 desde Aroer, que está al borde del valle de Arnón, y la ciudad que está en medio del valle, y toda la llanura de Medeba hasta Dibón;
Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
10 y todas las ciudades de Sehón, rey de los amorreos, que reinaba en Hesbón, hasta el límite de los hijos de Amón
da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
11 y Galaad, y el límite de los guesuritas y maacatitas, y todo el monte Hermón, y todo Basán hasta Salecá;
Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
12 todo el reino de Og en Basán, que reinaba en Astarot y en Edrei (que quedó del resto de los refaítas); porque Moisés atacó a éstos y los expulsó.
wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
13 Sin embargo, los hijos de Israel no expulsaron a los guesuritas ni a los maacatíes, sino que Guesur y Maacat viven dentro de Israel hasta el día de hoy.
Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
14 Sólo que no dio herencia a la tribu de Leví. Las ofrendas a Yahvé, el Dios de Israel, hechas por fuego, son su herencia, como él le dijo.
Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
15 Moisés dio a la tribu de los hijos de Rubén según sus familias.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
16 Su frontera fue desde Aroer, que está a la orilla del valle de Arnón, y la ciudad que está en medio del valle, y toda la llanura junto a Medeba;
Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
17 Hesbón, y todas sus ciudades que están en la llanura; Dibón, Bamoth Baal, Beth Baal Meón,
zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
18 Jahaz, Kedemoth, Mephaath,
Yahza, Kedemot, Mefa’at,
19 Kiriathaim, Sibmah, Zereth Shahar en el monte del valle,
Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
20 Beth Peor, las laderas de Pisga, Beth Jeshimoth,
Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
21 todas las ciudades de la llanura, y todo el reino de Sehón, rey de los amorreos, que reinaba en Hesbón, a quien Moisés hirió con los jefes de Madián, Evi, Rekem, Zur, Hur y Reba, príncipes de Sehón, que vivían en la tierra.
dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
22 Los hijos de Israel también mataron a espada a Balaam, hijo de Beor, el adivino, entre el resto de sus muertos.
Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
23 El límite de los hijos de Rubén era la ribera del Jordán. Esta fue la herencia de los hijos de Rubén según sus familias, las ciudades y sus aldeas.
Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
24 Moisés dio a la tribu de Gad, a los hijos de Gad, según sus familias.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
25 Su límite fue Jazer, y todas las ciudades de Galaad, y la mitad de la tierra de los hijos de Amón, hasta Aroer que está cerca de Rabá;
Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
26 y desde Hesbón hasta Ramat Mizpa, y Betonim; y desde Mahanaim hasta el límite de Debir
da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
27 y en el valle, Bet Haram, Bet Nimra, Sucot y Zafón, el resto del reino de Sehón, rey de Hesbón, la ribera del Jordán, hasta el extremo del mar de Cineret, al otro lado del Jordán, hacia el este.
kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
28 Esta es la herencia de los hijos de Gad según sus familias, las ciudades y sus aldeas.
Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
29 Moisés dio una herencia a la media tribu de Manasés. Fue para la media tribu de los hijos de Manasés según sus familias.
Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
30 Su frontera era desde Mahanaim, todo Basán, todo el reino de Og, rey de Basán, y todas las aldeas de Jair, que están en Basán, sesenta ciudades.
Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
31 La mitad de Galaad, Astarot y Edrei, ciudades del reino de Og en Basán, eran para los hijos de Maquir hijo de Manasés, para la mitad de los hijos de Maquir según sus familias.
da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
32 Estas son las herencias que Moisés repartió en las llanuras de Moab, al otro lado del Jordán, en Jericó, hacia el este.
Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
33 Pero Moisés no dio ninguna herencia a la tribu de Leví. Yahvé, el Dios de Israel, es su herencia, como él les habló.
Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.

< Josué 13 >