< Joel 2 >
1 Toca la trompeta en Sión, ¡y hacer sonar una alarma en mi montaña sagrada! Que tiemblen todos los habitantes de la tierra, porque llega el día de Yahvé, porque está muy cerca:
Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
2 Un día de oscuridad y penumbra, un día de nubes y espesa oscuridad. Como el amanecer que se extiende sobre las montañas, un pueblo grande y fuerte; nunca ha habido algo parecido, ni habrá más después de ellos, incluso a los años de muchas generaciones.
rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
3 Un fuego devora ante ellos, y detrás de ellos, arde una llama. La tierra es como el jardín del Edén ante ellos, y detrás de ellos, un desierto desolado. Sí, y nadie ha escapado de ellos.
A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
4 Su aspecto es como el de los caballos, y corren como jinetes.
Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
5 Como el ruido de los carros en las cimas de los montes, saltan, como el ruido de una llama de fuego que devora el rastrojo, como un pueblo fuerte puesto en orden de batalla.
Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
6 Ante su presencia los pueblos se angustian. Todos los rostros se han vuelto pálidos.
Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
7 Corren como hombres poderosos. Escalan el muro como guerreros. Cada uno de ellos marcha en su línea, y no se desvían del camino.
Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
8 Uno no empuja a otro. Cada uno marcha por su propio camino. Rompieron las defensas y no rompan filas.
Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
9 Se precipitan sobre la ciudad. Corren en la pared. Suben a las casas. Entran por las ventanas como ladrones.
Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
10 La tierra tiembla ante ellos. Los cielos tiemblan. El sol y la luna se oscurecen, y las estrellas retiran su brillo.
A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
11 Yahvé hace tronar su voz ante su ejército, porque sus fuerzas son muy grandes; porque es fuerte quien obedece su mandato; porque el día de Yahvé es grande y muy imponente, ¿y quién puede soportarlo?
Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
12 “Sin embargo, ahora mismo — dice Yahvé — vuélvete a mí con todo tu corazón, y con ayuno, llanto y luto”.
“Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
13 Rasga tu corazón y no tus vestiduras, y vuélvete a Yahvé, tu Dios; porque es clemente y misericordioso, lento para la ira, y abundante en bondad amorosa, y se abstiene de enviar la calamidad.
Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
14 ¿Quién sabe? Puede que se vuelva y ceda, y dejar una bendición detrás de él, una ofrenda de comida y una ofrenda de bebida a Yahvé, tu Dios.
Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
15 ¡Toca la trompeta en Sión! Santificar un ayuno. Convocar una asamblea solemne.
A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
16 Reúne al pueblo. Santificar la asamblea. Reúne a los ancianos. Reúne a los niños, y a los que amamantan de pecho. Que el novio salga de su habitación, y la novia fuera de su cámara.
A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
17 Que los sacerdotes, los ministros de Yahvé, lloren entre el pórtico y el altar, y que digan: “Perdona a tu pueblo, Yahvé, y no des tu herencia a los reproches, que las naciones se enseñoreen de ellos. ¿Por qué han de decir entre los pueblos, ¿Dónde está su Dios?”
Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
18 Entonces Yahvé se puso celoso por su tierra, y se apiadó de su pueblo.
Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
19 Yahvé respondió a su pueblo, “Mira, te enviaré grano, vino nuevo y aceite, y estarás satisfecho con ellos; y no volveré a hacer de ti un oprobio entre las naciones.
Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
20 Pero yo alejaré de ti al ejército del norte, y lo conducirá a una tierra estéril y desolada, su frente en el mar del este, y su espalda en el mar occidental; y su hedor surgirá, y su mal olor se elevará”. Seguro que ha hecho grandes cosas.
“Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
21 Tierra, no tengas miedo. Alegraos y regocijaos, porque Yahvé ha hecho grandes cosas.
Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
22 No tengáis miedo, animales del campo; porque los pastos del desierto brotan, porque el árbol da sus frutos. La higuera y la vid dan su fuerza.
Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
23 “Alegraos, pues, hijos de Sión, y alégrate en Yahvé, tu Dios; pues te da la lluvia temprana en justa medida, y hace que la lluvia caiga para ti, la lluvia temprana y la lluvia tardía, como antes.
Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
24 Las eras estarán llenas de trigo, y las cubas rebosarán de vino nuevo y aceite.
Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
25 Te devolveré los años que se ha comido la langosta, la gran langosta, el saltamontes y la oruga, mi gran ejército, que envié entre vosotros.
“Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
26 Tendrás mucho que comer y estarás satisfecho, y alabarán el nombre de Yahvé, su Dios, que ha tratado maravillosamente contigo; y mi pueblo nunca más será decepcionado.
Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
27 Sabrás que estoy en medio de Israel, y que yo soy Yahvé, tu Dios, y no hay otro; y mi pueblo nunca más será decepcionado.
Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
28 “Después sucederá que derramaré mi Espíritu sobre toda la carne; y tus hijos y tus hijas profetizarán. Tus viejos soñarán sueños. Sus jóvenes verán visiones.
“Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
29 Y también sobre los siervos y las siervas en aquellos días, Derramaré mi Espíritu.
Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
30 Mostraré maravillas en los cielos y en la tierra: sangre, fuego y columnas de humo.
Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
31 El sol se convertirá en oscuridad, y la luna en sangre, antes de que llegue el gran y terrible día de Yahvé.
Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
32 Sucederá que quien invoque el nombre de Yahvé se salvará; porque en el monte Sión y en Jerusalén habrá quienes escapen, como ha dicho Yahvé, y entre el remanente, los que Yahvé llama.
Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.