< Job 9 >

1 Entonces Job respondió,
Sai Ayuba ya amsa,
2 “En verdad sé que es así, ¿pero cómo puede el hombre ser justo con Dios?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 Si se complace en contender con él, no puede responderle ni una vez entre mil.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Dios es sabio de corazón y poderoso de fuerza. ¿Quién se ha endurecido contra él y ha prosperado?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 Él remueve las montañas, y ellos no lo saben, cuando los derriba en su cólera.
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 Sacude la tierra de su lugar. Sus pilares tiemblan.
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 Ordena el sol y no sale, y sella las estrellas.
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 Sólo él extiende los cielos, y pisa las olas del mar.
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 Él hace la Osa, Orión y las Pléyades, y las habitaciones del sur.
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 Él hace grandes cosas más allá de descubrirlas; sí, cosas maravillosas sin número.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 He aquí que pasa por delante de mí y no lo veo. También pasa, pero no lo percibo.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 He aquí que él arrebata. ¿Quién puede impedirlo? ¿Quién le preguntará: “Qué estás haciendo?”?
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 “Dios no retirará su ira. Los ayudantes de Rahab se inclinan bajo él.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 Cuánto menos le responderé, y elegir mis palabras para discutir con él?
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 Aunque fuera justo, no le respondería. Yo haría una súplica a mi juez.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Si yo hubiera llamado, y él me hubiera respondido, sin embargo, no creo que haya escuchado mi voz.
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 Porque me rompe con una tormenta, y multiplica mis heridas sin causa.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 No me permite recuperar el aliento, pero me llena de amargura.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 Si se trata de una cuestión de fuerza, ¡he aquí que él es poderoso! Si de justicia se trata, “¿Quién — dice — me va a convocar?”.
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Aunque sea justo, mi propia boca me condenará. Aunque sea intachable, se demostrará que soy perverso.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 Soy irreprochable. No me respeto a mí mismo. Desprecio mi vida.
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 “Todo es lo mismo. Por eso digo que destruye a los irreprochables y a los malvados.
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 Si el azote mata de repente, se burlará en el juicio de los inocentes.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 La tierra es entregada a la mano de los malvados. Cubre los rostros de sus jueces. Si no es él, ¿quién es?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 “Ahora mis días son más rápidos que un corredor. Huyen. No ven nada bueno.
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 Han pasado como las naves rápidas, como el águila que se abalanza sobre la presa.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 Si digo: ‘Olvidaré mi queja’, Voy a quitar mi cara de tristeza y a animarme”.
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 Tengo miedo de todas mis penas. Sé que no me considerará inocente.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 Seré condenado. ¿Por qué entonces trabajo en vano?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 Si me lavo con nieve y limpiar mis manos con lejía,
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 sin embargo, me hundirás en la zanja. Mi propia ropa me aborrecerá.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 Porque él no es un hombre como yo, para que le responda, que debemos reunirnos en el juicio.
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 No hay árbitro entre nosotros, que podría poner su mano sobre nosotros dos.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Que me quite la vara. Que su terror no me haga temer;
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 entonces hablaría y no le temería, pues no lo soy en mí mismo.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Job 9 >