< Job 39 >
1 “¿Sabéis en qué momento paren las cabras montesas? ¿Observas cuando la cierva tiene cervatillo?
“Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
2 ¿Puedes contar los meses que cumplen? ¿O sabes la hora en que dan a luz?
Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
3 Se inclinan. Llevan a sus crías. Terminan sus dolores de parto.
Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
4 Sus crías se hacen fuertes. Crecen en el campo abierto. Salen y no vuelven.
’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
5 “¿Quién ha liberado al burro salvaje? O que ha soltado las amarras del asno veloz,
“Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
6 cuyo hogar he convertido en el desierto, y la tierra salada su morada?
Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
7 Desprecia el tumulto de la ciudad, tampoco oye los gritos del conductor.
Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
8 La cordillera es su pasto. Busca cada cosa verde.
Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
9 “¿Se contentará el buey salvaje con servirte? ¿O se quedará junto a tu comedero?
“Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
10 ¿Puedes sujetar al buey salvaje en el surco con su arnés? ¿O va a labrar los valles después de ti?
Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
11 ¿Confiarás en él, porque su fuerza es grande? ¿O le dejarás tu trabajo?
Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
12 ¿Confiarás en él para que traiga a casa tu semilla? y recoger el grano de tu era?
Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
13 “Las alas del avestruz se agitan con orgullo, ¿pero son las plumas y el plumaje del amor?
“Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
14 Porque deja sus huevos en la tierra, los calienta en el polvo,
Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
15 y olvida que el pie puede aplastarlos, o que el animal salvaje los pisotee.
ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
16 Trata con dureza a sus crías, como si no fueran suyas. Aunque su trabajo es en vano, no tiene miedo,
Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
17 porque Dios la ha privado de sabiduría, tampoco le ha impartido entendimiento.
Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
18 Cuando se eleva a lo alto, desprecia al caballo y a su jinete.
Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
19 “¿Le has dado fuerza al caballo? ¿Has vestido su cuello con una melena temblorosa?
“Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
20 ¿Le has hecho saltar como una langosta? La gloria de su resoplido es impresionante.
Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
21 Pisa el valle y se regocija en su fuerza. Sale al encuentro de los hombres armados.
Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
22 Se burla del miedo y no se amilana, ni se aparta de la espada.
Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
23 El carcaj se sacude contra él, la lanza y la jabalina.
Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
24 Come la tierra con fiereza y rabia, ni se queda quieto al sonido de la trompeta.
Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
25 Cada vez que suena la trompeta, resopla: “¡Ah! Huele la batalla a lo lejos, el estruendo de los capitanes, y los gritos.
Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
26 “¿Es por tu sabiduría que el halcón vuela, y extiende sus alas hacia el sur?
“Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
27 ¿Es por tu orden que el águila se levanta, y hace su nido en las alturas?
Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
28 En el acantilado habita y hace su hogar, en la punta del acantilado y la fortaleza.
Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
29 Desde allí espía la presa. Sus ojos lo ven de lejos.
Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
30 Sus crías también chupan sangre. Donde están los muertos, allí está él”.
’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”