< Job 34 >
1 Además, Eliú respondió,
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 “Escuchad mis palabras, sabios. Escúchame, tú que tienes conocimiento.
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 Porque el oído prueba las palabras, como el paladar prueba la comida.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Escojamos para nosotros lo que es correcto. Conozcamos entre nosotros lo que es bueno.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 Porque Job ha dicho: “Soy justo”, Dios me ha quitado el derecho.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 A pesar de mi derecho se me considera un mentiroso. Mi herida es incurable, aunque estoy sin desobediencia’.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Qué hombre es como Job, que bebe el desprecio como el agua,
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 que va en compañía de los obreros de la iniquidad, y camina con los hombres malvados?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 Porque él ha dicho: “De nada le sirve al hombre para que se deleite con Dios”.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 “Por tanto, escuchadme, hombres de entendimiento: lejos de Dios, que haga la maldad, del Todopoderoso, para que cometa iniquidad.
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 Porque el trabajo de un hombre se lo devolverá, y haz que cada uno encuentre según sus caminos.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Sí, ciertamente, Dios no hará maldad, ni el Todopoderoso pervertirá la justicia.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 ¿Quién lo puso a cargo de la tierra? ¿O quién lo ha designado sobre el mundo entero?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 Si pone su corazón en sí mismo, si reuniera para sí su espíritu y su aliento,
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 toda la carne perecería junta, y el hombre volvería a convertirse en polvo.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 “Si ahora tienes entendimiento, escucha esto. Escucha la voz de mis palabras.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 ¿Debe gobernar incluso quien odia la justicia? ¿Condenarás al que es justo y poderoso,
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 que dice a un rey: “¡Vil! o a los nobles, “¡malvados!”?
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 No respeta las personas de los príncipes, ni respetar a los ricos más que a los pobres, porque todos son obra de sus manos.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 En un momento mueren, incluso a medianoche. El pueblo se estremece y fallece. A los poderosos se les quita la mano.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 “Porque sus ojos están en los caminos del hombre. Él ve todas sus salidas.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 No hay oscuridad, ni tinieblas espesas, donde los obreros de la iniquidad pueden esconderse.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 Porque no necesita considerar más a un hombre, que debe ir ante Dios en el juicio.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 El rompe en pedazos a los hombres poderosos de una manera que no se puede descubrir, y pone a otros en su lugar.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Por eso toma conocimiento de sus obras. Él los derriba en la noche, para que sean destruidos.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 Los golpea como hombres malvados a la vista de los demás;
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 porque se apartaron de seguirlo, y no prestaba atención a ninguna de sus formas,
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 de modo que hicieron llegar a él el clamor de los pobres. Oyó el clamor de los afligidos.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Cuando da tranquilidad, ¿quién puede entonces condenar? Cuando esconde su rostro, ¿quién puede verlo entonces? Está sobre una nación o un hombre por igual,
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 para que no reine el hombre impío, para que no haya nadie que engañe al pueblo.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 “Porque ¿ha dicho alguno a Dios, ‘Soy culpable, pero no ofenderé más.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Enséñame lo que no veo. Si he hecho iniquidad, no la haré más’?
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 ¿Será su recompensa como deseas, que la rechaces? Porque tú debes elegir, y no yo. Por lo tanto, habla de lo que sabes.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Los hombres de entendimiento me dirán, sí, todo sabio que me escuche:
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 “Job habla sin conocimiento. Sus palabras carecen de sabiduría”.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 Deseo que Job sea juzgado hasta el final, a causa de su respuesta como hombres malvados.
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 Porque añade la rebelión a su pecado. Aplaude entre nosotros, y multiplica sus palabras contra Dios”.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”