< Job 32 >

1 Así que estos tres hombres dejaron de responder a Job, porque era justo a sus ojos.
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
2 Entonces se encendió la ira de Elihú, hijo de Baraquel, buzita, de la familia de Ram, contra Job. Su ira se encendió porque él se justificaba a sí mismo antes que a Dios.
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
3 También se encendió su ira contra sus tres amigos, porque no habían encontrado respuesta, y sin embargo habían condenado a Job.
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
4 Ahora bien, Elihú había esperado para hablar con Job, porque ellos eran mayores que él.
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
5 Cuando Elihú vio que no había respuesta en la boca de estos tres hombres, se encendió su ira.
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
6 Eliú, hijo de Baraquel, el buzita, respondió, “Yo soy joven, y tú eres muy viejo. Por eso me contuve y no me atreví a mostrarte mi opinión.
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
7 Dije: “Los días deben hablar, y la multitud de años debe enseñar la sabiduría”.
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
8 Pero hay un espíritu en el hombre, y el Espíritu del Todopoderoso les da entendimiento.
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
9 No son los grandes los que son sabios, ni a los ancianos que entienden de justicia.
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
10 Por eso le dije: “Escúchame; Yo también mostraré mi opinión”.
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
11 “He aquí que he esperado tus palabras, y escuché su razonamiento, mientras buscabas qué decir.
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
12 Sí, te he prestado toda mi atención, pero no hubo nadie que convenciera a Job, o que respondió a sus palabras, entre vosotros.
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
13 Tened cuidado, no sea que digáis: “Hemos encontrado la sabiduría”. Dios puede refutarlo, no el hombre;’
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
14 pues no ha dirigido sus palabras contra mí; tampoco le responderé con sus discursos.
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
15 “Están asombrados. No responden más. No tienen nada que decir.
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16 ¿Debo esperar, porque ellos no hablan, porque se quedan quietos y no responden más?
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17 Yo también responderé a mi parte, y también mostraré mi opinión.
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18 Porque estoy lleno de palabras. El espíritu dentro de mí me constriñe.
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19 He aquí que mi pecho es como el vino que no tiene salida; como los odres nuevos, está a punto de reventar.
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20 Voy a hablar para que me refresquen. Abriré mis labios y responderé.
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21 Por favor, no permitas que respete la persona de ningún hombre, ni daré títulos lisonjeros a ningún hombre.
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22 Porque no sé dar títulos halagadores, o si no, mi Hacedor me llevaría pronto.
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.

< Job 32 >