< Job 30 >
1 “Pero ahora los que son más jóvenes que yo se burlan de mí, cuyos padres consideré indignos de poner con mis perros pastores.
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 ¿De qué me sirve la fuerza de sus manos? hombres en los que la edad madura ha perecido?
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 Están demacrados por la carencia y el hambre. Roen la tierra seca, en la penumbra del desperdicio y la desolación.
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 Arrancan hierbas saladas junto a los arbustos. Las raíces del árbol de la retama son su alimento.
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 Son expulsados de entre los hombres. Lloran tras ellos como tras un ladrón,
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 para que vivan en valles espantosos, y en agujeros de la tierra y de las rocas.
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 Rebuznan entre los arbustos. Están reunidos bajo las ortigas.
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 Son hijos de locos, sí, hijos de malvados. Fueron expulsados a latigazos de la tierra.
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 “Ahora me he convertido en su canción. Sí, soy un sinónimo para ellos.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 Me aborrecen, se alejan de mí, y no duden en escupirme a la cara.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 Porque ha desatado su cuerda y me ha afligido; y se han desprendido de la restricción ante mí.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 A mi derecha se levanta la chusma. Me apartan los pies. Ellos lanzan sus caminos de destrucción contra mí.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 Marcan mi camino. Promueven mi destrucción sin la ayuda de nadie.
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 Como a través de una amplia brecha llegan. Se enrollan en medio de la ruina.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 Los terrores se han vuelto contra mí. Persiguen mi honor como el viento. Mi bienestar ha pasado como una nube.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 “Ahora mi alma se derrama dentro de mí. Los días de aflicción se han apoderado de mí.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 En la estación nocturna mis huesos están calados en mí, y los dolores que me roen no tienen descanso.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 Mi vestimenta está desfigurada por una gran fuerza. Me ata como el cuello de mi túnica.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 Me ha arrojado al fango. Me he convertido en polvo y cenizas.
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 Clamo a ti, y no me respondes. Me pongo de pie, y tú me miras.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 Te has vuelto cruel conmigo. Con la fuerza de tu mano me persigues.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 Me alzas al viento y me conduces con él. Me disuelves en la tormenta.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 Porque sé que me llevarás a la muerte, a la casa designada para toda la vida.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 “Sin embargo, ¿no se tiende la mano en su caída? ¿O en su calamidad, por tanto, clamar por ayuda?
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 ¿No lloré por el que estaba en apuros? ¿No se afligió mi alma por los necesitados?
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 Cuando buscaba el bien, vino el mal. Cuando esperaba la luz, llegó la oscuridad.
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 Mi corazón está turbado y no descansa. Me han llegado días de aflicción.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 Voy de luto sin el sol. Me pongo de pie en la asamblea y pido ayuda.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 Soy hermano de los chacales, y compañera de los avestruces.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 Mi piel se ennegrece y se desprende de mí. Mis huesos están quemados por el calor.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 Por eso mi arpa se ha convertido en luto, y mi pipa en la voz de los que lloran.
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.