< Job 27 >
1 Job retomó su parábola y dijo
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 “Vive Dios, que me ha quitado el derecho, el Todopoderoso, que ha amargado mi alma
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 (por la duración de mi vida aún está en mí, y el espíritu de Dios está en mis narices);
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 ciertamente mis labios no hablarán injusticia, ni mi lengua proferirá engaños.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 Lejos de mí el justificaros. Hasta que no muera no apartaré mi integridad de mí.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 Me aferro a mi justicia y no la abandono. Mi corazón no me reprochará mientras viva.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 “Que mi enemigo sea como el malvado. Que el que se levante contra mí sea como los injustos.
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 Porque ¿cuál es la esperanza del impío, cuando es cortado? cuando Dios le quita la vida?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 ¿Oirá Dios su clamor cuando le sobrevengan problemas?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 Se deleitará en el Todopoderoso, e invocar a Dios en todo momento?
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 Te enseñaré sobre la mano de Dios. No ocultaré lo que está con el Todopoderoso.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 Mirad, todos vosotros lo habéis visto; ¿por qué entonces te has vuelto totalmente vanidoso?
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 “Esta es la porción de un hombre malvado con Dios, la herencia de los opresores, que reciben del Todopoderoso.
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 Si sus hijos se multiplican, es por la espada. Su descendencia no se conformará con el pan.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 Los que queden de él serán enterrados en la muerte. Sus viudas no se lamentarán.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 Aunque amontone plata como el polvo, y preparar la ropa como la arcilla;
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 puede prepararlo, pero el justo se lo pondrá, y los inocentes se repartirán la plata.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 Construye su casa como la polilla, como una caseta que hace el vigilante.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 Se acuesta rico, pero no volverá a hacerlo. Abre los ojos y no está.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 Los terrores lo alcanzan como las aguas. Una tormenta se lo lleva en la noche.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 El viento del este lo arrastra y se va. Lo barre de su lugar.
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 Porque se lanza contra él y no perdona, mientras huye de su mano.
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 Los hombresle aplaudirán, y lo sacará de su lugar con un silbido.
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”