< Job 21 >

1 Entonces Job respondió,
Sai Ayuba ya amsa,
2 “Escucha con atención mi discurso. Que esto te sirva de consuelo.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Permíteme, y yo también hablaré. Después de que yo haya hablado, burlate.
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 En cuanto a mí, ¿es mi queja ante el hombre? ¿Por qué no debería estar impaciente?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Mírame y asómbrate. Pon la mano en la boca.
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Cuando me acuerdo, me siento turbado. El horror se apodera de mi carne.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 “¿Por qué viven los malvados? ¿envejecer, sí, y hacerse poderoso en el poder?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Su hijo está establecido con ellos ante sus ojos, su descendencia ante sus ojos.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Sus casas están a salvo del miedo, ni la vara de Dios sobre ellos.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Sus toros se reproducen sin falta. Sus vacas paren y no abortan.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 Envían a sus pequeños como un rebaño. Sus hijos bailan.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 Cantan al son de la pandereta y el arpa, y se regocijan con el sonido de la pipa.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Pasan sus días en la prosperidad. En un instante bajan al Seol. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 Le dicen a Dios: “Apártate de nosotros”, porque no queremos saber de tus costumbres.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 ¿Qué es el Todopoderoso, para que le sirvamos? ¿Qué provecho vamos a tener si le rezamos?
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 He aquí que su prosperidad no está en su mano. El consejo de los malvados está lejos de mí.
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 “Cuántas veces se apaga la lámpara de los impíos, que su calamidad venga sobre ellos, que Dios reparte penas en su ira?
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 Cuántas veces son como rastrojos ante el viento, como paja que se lleva la tormenta?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 Dices: “Dios hace recaer su iniquidad sobre sus hijos”. Que se recompense a sí mismo, para que lo sepa.
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 Que sus propios ojos vean su destrucción. Que beba de la ira del Todopoderoso.
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Pues qué le importa su casa después de él, cuando el número de sus meses se corta?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 “¿Alguien enseñará el conocimiento de Dios, ya que juzga a los que están en lo alto?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 Uno muere con todas sus fuerzas, estando totalmente a gusto y tranquilo.
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 Sus cubos están llenos de leche. La médula de sus huesos se humedece.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 Otro muere en la amargura del alma, y nunca sabe bien.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Se acuestan por igual en el polvo. El gusano los cubre.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 “He aquí que conozco tus pensamientos, los planes con los que me equivocas.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 Porque decís: “¿Dónde está la casa del príncipe? ¿Dónde está la tienda en la que vivían los malvados?
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 ¿No has preguntado a los caminantes? ¿No conoces sus evidencias?
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 que el hombre malo está reservado para el día de la calamidad, que son llevados al día de la ira?
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 ¿Quién declarará su camino a la cara? ¿Quién le pagará lo que ha hecho?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Sin embargo, será llevado a la tumba. Los hombres vigilarán la tumba.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 Los terrones del valle serán dulces para él. Todos los hombres irán detrás de él, como hubo innumerables antes de él.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Así quecómo puedes consolarme con tonterías, porque en sus respuestas sólo queda la falsedad”.
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >