< Job 10 >

1 “Mi alma está cansada de mi vida. Daré curso libre a mi queja. Hablaré con la amargura de mi alma.
“Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
2 Le diré a Dios: “No me condenes. Muéstrame por qué contiendes conmigo.
Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
3 ¿Es bueno para ti que oprimas, que desprecies el trabajo de tus manos, y sonreír al consejo de los malvados?
Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
4 ¿Tienes ojos de carne? ¿O ves como ve el hombre?
Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
5 Son tus días como los de los mortales, o tus años como los del hombre,
Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
6 que indaguen en mi iniquidad, ¿y buscar mi pecado?
da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
7 Aunque sabes que no soy malvado, no hay nadie que pueda liberar de su mano.
Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
8 “‘Tus manos me han enmarcado y me han formado por completo, y sin embargo me destruyes.
“Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
9 Acuérdate, te lo ruego, de que me has formado como el barro. ¿Volverás a convertirme en polvo?
Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
10 No me has derramado como la leche, y me cuajó como un queso?
Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
11 Me has vestido de piel y carne, y me unió con huesos y tendones.
Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
12 Me has concedido la vida y la bondad amorosa. Su visita ha preservado mi espíritu.
Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
13 Sin embargo, escondiste estas cosas en tu corazón. Sé que esto es contigo:
“Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
14 si peco, entonces me marcas. No me absolverás de mi iniquidad.
In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
15 Si soy malvado, ay de mí. Si soy justo, todavía no levantaré la cabeza, llenándose de desgracia, y consciente de mi aflicción.
Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
16 Si mi cabeza está en alto, me cazan como a un león. De nuevo te muestras poderoso ante mí.
In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
17 Renováis vuestros testigos contra mí, y aumentar su indignación sobre mí. Los cambios y la guerra están conmigo.
Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
18 “‘¿Por qué, pues, me has sacado del vientre? Ojalá hubiera renunciado al espíritu, y ningún ojo me hubiera visto.
“Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
19 debería haber sido como si no lo hubiera sido. Debería haber sido llevado desde el vientre a la tumba.
Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
20 ¿No son pocos mis días? ¡Para! Dejadme en paz, para que pueda encontrar un poco de consuelo,
’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
21 antes de ir a donde no volveré, a la tierra de las tinieblas y de la sombra de la muerte;
kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
22 la tierra oscura como la medianoche, de la sombra de la muerte, sin ningún tipo de orden, donde la luz es como la medianoche”.
zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”

< Job 10 >