< Jeremías 50 >
1 La palabra que Yahvé habló sobre Babilonia, sobre la tierra de los caldeos, por medio del profeta Jeremías.
Ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Irmiya annabi game da Babilon da kuma ƙasar Babiloniyawa.
2 “Anunciad entre las naciones y publicad, y establecer una norma; publicar, y no ocultar; dicen, ‘Babilonia ha sido tomada, Bel está decepcionada, ¡Merodach está consternado! Sus imágenes son decepcionantes. Sus ídolos están consternados’.
“Ka yi shela ka kuma furta a cikin al’ummai, ka tā da tuta ka kuma furta; kada ku ɓoye kome, amma ku ce, ‘Za a ci Babilon da yaƙi; za a kunyata Bel, Marduk ya cika da tsoro. Siffofinta za su sha kunya gumakanta za su cika da tsoro.’
3 Porque una nación sube del norte contra ella, que hará que su tierra quede desolada, y nadie habitará en ella. Han huido. Se han ido, tanto del hombre como del animal.
Al’umma daga arewa za tă fāɗa mata su mai da ƙasar kango. Ba wanda zai zauna a cikinta; mutane da dabbobi za su gudu.
4 “En aquellos días y en aquel tiempo”, dice Yahvé, “Los hijos de Israel vendrán, ellos y los hijos de Judá juntos; seguirán su camino llorando, y buscarán a Yahvé, su Dios.
“A kwanakin nan, a wannan lokaci,” in ji Ubangiji, “mutanen Isra’ila da mutanen Yahuda gaba ɗaya za su tafi cikin hawaye su nemi Ubangiji Allahnsu.
5 Preguntarán por Sión con el rostro vuelto hacia ella, diciendo: “Venid y uníos a Yahvé en un pacto eterno que no será olvidado”.
Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su kuma juya fuskokinsu wajenta. Za su zo su haɗa kansu ga Ubangiji a madawwamin alkawari da ba za a manta da shi ba.
6 Mi pueblo ha sido una oveja perdida. Sus pastores les han hecho extraviarse. Los han rechazado en las montañas. Han pasado de la montaña a la colina. Han olvidado su lugar de descanso.
“Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
7 Todos los que los encontraron los devoraron. Sus adversarios dijeron: ‘No somos culpables’, porque han pecado contra Yahvé, la morada de la justicia, el Señor, la esperanza de sus padres”.
Duk wanda ya same su ya cinye su; abokan gābansu suka ce, ‘Ba mu da laifi, gama sun yi zunubi wa Ubangiji, wurin kiwonsu na gaske, Ubangiji, abin sa zuciyar kakanninsu.’
8 “¡Huye de en medio de Babilonia! Sal de la tierra de los caldeos, y ser como los machos cabríos ante los rebaños.
“Ku gudu daga Babilon; ku bar ƙasar Babiloniyawa, ku zama kamar awakin da suke bi da garke.
9 Porque, he aquí que voy a suscitar y haz subir contra Babilonia una compañía de grandes naciones del país del norte; y se pondrán en fila contra ella. Se la llevarán de allí. Sus flechas serán como las de un poderoso experto. Ninguno de ellos volverá en vano.
Gama zan kuta in kuma kawo a kan Babilon haɗinkan manyan al’ummai na arewa. Za su ja dāgār gāba da ita, kuma daga arewa za a ci ta da yaƙi. Kibiyoyinsu za su zama kamar na gwanayen jarumawa waɗanda ba sa dawowa hannu wofi.
10 Caldea será una presa. Todos los que se aprovechan de ella quedarán satisfechos”, dice Yahvé.
Saboda haka za a washe Babiloniyawa; dukan waɗanda suka washe ta za su ƙoshi,” in ji Ubangiji.
11 “Porque te alegras, porque te alegras, Oh, tú que saqueas mi herencia, porque eres licenciosa como una vaquilla que pisa el grano, y relinchar como caballos fuertes,
“Saboda kuna farin ciki kuna kuma murna, ku da kuka washe gādona, domin kuna tsalle kamar karsana mai sussuka hatsi kuna kuma haniniya kamar ingarmu.
12 tu madre estará totalmente decepcionada. La que te parió será confundida. He aquí que ella será la más pequeña de las naciones, un desierto, una tierra árida y una zona desértica.
Mahaifiyarku za tă sha babbar kunya; ita da ta haife ku za tă sha kunya. Za tă zama mafi ƙanƙanta na al’ummai, jeji, busasshiyar ƙasa, hamada.
13 A causa de la ira de Yahvé no será habitada, pero estará totalmente desolada. Todos los que pasen por Babilonia se quedarán asombrados, y sisea en todas sus plagas.
Saboda fushin Ubangiji ba za tă zauna a cikinta ba amma za tă zama kufai gaba ɗaya. Duk waɗanda suka wuce Babilon za su ji tsoro su kuma yi tsaki saboda dukan mikinta.
14 Poneos en guardia contra Babilonia por todas partes, a todos los que doblan el arco; disparar contra ella. No escatimes en flechas, porque ha pecado contra Yahvé.
“Ku ja dāgā kewaye da Babilon, dukanku waɗanda kuke jan baka. Ku harbe ta! Kada ku rage kibiyoyi, gama ta yi zunubi ga Ubangiji.
15 Griten contra ella todos. Se ha sometido a sí misma. Sus baluartes han caído. Sus muros han sido derribados, porque es la venganza de Yahvé. Véngate de ella. Como ella ha hecho, hazle a ella.
Ku yi kuwwa a kanta a kowane gefe! Ta miƙa wuya, hasumiyarta ta fāɗi, katangarta sun rushe. Da yake wannan sakayya ce ta Ubangiji, ku ɗauki fansa a kanta; yi mata yadda ta yi wa waɗansu.
16 Corta el sembrador de Babilonia, y el que maneja la hoz en el tiempo de la cosecha. Por miedo a la espada opresora, cada uno de ellos regresará a su propio pueblo, y cada uno huirá a su tierra.
Ku datse wa Babilon mai shuka, da mai girbi lauje a lokacin girbi. Saboda takobin mai zalunci bari kowa ya koma ga mutanensa, bari kowa ya gudu zuwa ga ƙasarsa.
17 “Israel es una oveja cazada. Los leones lo han ahuyentado. Primero, el rey de Asiria lo devoró, y ahora por fin Nabucodonosor, rey de Babilonia, le ha roto los huesos”.
“Isra’ila garke ne da ya watse da zakoki suka kora. Na farkon da ya cinye shi sarkin Assuriya ne; na ƙarshen da ya ragargaza ƙasusuwansa Nebukadnezzar sarkin Babilon ne.”
18 Por eso dice el Señor de los Ejércitos, el Dios de Israel: “He aquí que yo castigaré al rey de Babilonia y a su tierra, como he castigado al rey de Asiria.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Zan hukunta sarkin Babilon da ƙasarsa yadda na hukunta sarkin Assuriya.
19 Volveré a llevar a Israel a sus pastos, y se alimentará del Carmelo y del Basán. Su alma será satisfecha en las colinas de Efraín y en Galaad.
Amma zan komo da Isra’ila zuwa wurin kiwonsa zai kuwa yi kiwo a Karmel da Bashan; zai ƙosar da marmarinsa a tuddan Efraim da Gileyad.
20 En aquellos días y en aquel tiempo”, dice Yahvé, “la iniquidad de Israel será buscada, y no habrá ninguno, también los pecados de Judá, y no se encontrarán; porque yo perdonaré a los que deje como remanente.
A kwanakin nan, da kuma a lokacin nan,” in ji Ubangiji, “za a yi bincike don laifin Isra’ila, amma ba za a samu ba, kuma don zunubin Yahuda, amma ba za a sami wani abu ba, gama zan gafarta wa raguwar da na rage.
21 “Sube contra la tierra de Merathaim, incluso contra ella, y contra los habitantes de Pekod. Maten y destruyan por completo después de ellos”, dice Yahvé, “y haced todo lo que os he mandado.
“Ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da waɗanda suke zama a Fekod. Ku fafara, ku kashe kuma hallaka su sarai,” in ji Ubangiji. “Ku aikata dukan abin da na umarce ku.
22 Un sonido de batalla está en la tierra, y de gran destrucción.
Hargowar yaƙi tana a ƙasar, hargowar babbar hallaka!
23 ¡Cómo se corta y se rompe el martillo de toda la tierra! ¡Cómo se ha convertido Babilonia en una desolación entre las naciones!
Dubi yadda aka karya aka kuma ragargaza gudumar dukan duniya! Dubi yadda Babilon ta zama kufai a cikin al’ummai!
24 Te he tendido una trampa, y tú también estás tomada, Babilonia, y tú no eras consciente. Te han encontrado, y también se ha capturado, porque has luchado contra Yahvé.
Na sa miki tarko, Babilon, kika kuwa kamu kafin ki sani; aka same ki aka kuma kama ki domin kin tayar wa Ubangiji.
25 Yahvé ha abierto su arsenal, y ha sacado las armas de su indignación; porque el Señor, Yahvé de los Ejércitos, tiene una obra que hacer en la tierra de los caldeos.
Ubangiji ya buɗe taskar makamansa ya fitar da makaman fushinsa, gama Maɗaukaki Ubangiji Mai Iko Duka yana da aikin da zai yi a ƙasar Babiloniyawa.
26 Vengan contra ella desde la frontera más lejana. Abre sus almacenes. Echadla como si fuera un montón. Destrúyela por completo. Que no quede nada de ella.
Ku zo ku yi gāba da ita daga nesa. Ku buɗe rumbunanta; ku jibga ta kamar tsibin hatsi. Ku hallaka ta sarai kada ku bar mata raguwa.
27 Mata a todos sus toros. Que vayan al matadero. ¡Ay de ellos! Porque su día ha llegado, el momento de su visita.
Ku kashe dukan’yan bijimanta bari su gangara zuwa mayanka! Kaitonsu! Gama ranansu ta zo, lokaci ya yi da za a hukunta su.
28 Escucha a los que huyen y escapan de la tierra de Babilonia, para anunciar en Sión la venganza de Yahvé, nuestro Dios, la venganza de su templo.
Ku saurari masu gudun hijira da masu neman mafaka daga Babilon suna furtawa a Sihiyona yadda Ubangiji Allahnmu ya ɗauki fansa, fansa domin haikalinsa.
29 “Convoca a los arqueros contra Babilonia, todos los que doblan el arco. Acampa contra ella por todos lados. Que no se le escape nada. Págale de acuerdo a su trabajo. De acuerdo con todo lo que ha hecho, hazle; porque se ha ensoberbecido contra Yahvé, contra el Santo de Israel.
“Ku kira’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
30 Por eso sus jóvenes caerán en sus calles. Todos sus hombres de guerra serán silenciados en ese día”, dice Yahvé.
Saboda haka, samarinta za su fāɗi a tituna; za a kawar da dukan sojojinta a wannan rana,” in ji Ubangiji.
31 “He aquí que estoy contra ti, soberbio”, dice el Señor, Yahvé de los Ejércitos; “porque su día ha llegado, la hora en que te visitaré.
“Ga shi, ina gāba da ke, ya ke mai girman kai,” in ji Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, “gama ranarki ta zo, lokacin da za a hukunta ki.
32 El orgulloso tropezará y caerá, y nadie lo levantará. Encenderé un fuego en sus ciudades, y devorará a todos los que estén a su alrededor”.
Mai ɗaga kai za tă yi tuntuɓe ta kuma fāɗi kuma ba wanda zai taimake ta tă tashi; zan hura wuta a garuruwanta da za tă cinye duk waɗanda suke kewaye da ita.”
33 El Señor de los Ejércitos dice: “Los hijos de Israel y los hijos de Judá están oprimidos juntos. Todos los que los tomaron cautivos los retienen. Se niegan a dejarlos ir.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “An danne mutanen Isra’ila, haka ma mutanen Yahuda. Dukan waɗanda suka kama su suna riƙe su kankan, suna kin barinsu su tafi.
34 Su Redentor es fuerte. Yahvé de los Ejércitos es su nombre. Defenderá a fondo su causa, para dar descanso a la tierra, y perturbar a los habitantes de Babilonia.
Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.
35 “Una espada está sobre los caldeos”, dice Yahvé, “y sobre los habitantes de Babilonia, en sus príncipes, y en sus sabios.
“Akwai takobi a kan Babiloniyawa!” In ji Ubangiji “a kan waɗanda suke zama a Babilon da kuma a kan fadawanta da masu hikimarta!
36 Una espada está sobre los fanfarrones, y se convertirán en tontos. Una espada está sobre sus poderosos hombres, y estarán consternados.
Akwai takobi a kan annabawan ƙaryanta! Za su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta! Za su cika da tsoro.
37 Una espada está sobre sus caballos, en sus carros, y en todas las personas mixtas que están en medio de ella; y se convertirán en mujeres. Una espada está en sus tesoros, y serán robados.
Akwai takobi a kan dawakanta da kekunan yaƙinta da kuma dukan baƙin da suke cikin mayaƙanta! Za su zama mata. Akwai takobi a kan dukiyarta! Za a washe su.
38 Una sequía está sobre sus aguas, y se secarán; porque es una tierra de imágenes grabadas, y están locos por los ídolos.
Fări a kan ruwanta! Za su bushe ƙaf. Gama ƙasa ce ta gumaka, gumakan da za su haukace da tsoro.
39 Por eso los animales salvajes del desierto con los lobos morarán allí. Las avestruces habitarán en ella. Ya no será habitada para siempre, tampoco se vivirá de generación en generación.
“Saboda haka halittun hamada da kuraye za su zauna a can, a can kuma mujiya za tă zauna. Ba za a ƙara zauna ko a yi zama a cikinta ba daga tsara zuwa tsara.
40 Como cuando Dios derribó a Sodoma y Gomorra y a sus ciudades vecinas”, dice Yahvé, “para que ningún hombre habite allí, ni ningún hijo de hombre vivirá en ella.
Yadda Allah ya tumɓuke Sodom da Gomorra tare da maƙwabtan garuruwansu,” in ji Ubangiji “haka ma ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
41 “He aquí que un pueblo viene del norte. Una gran nación y muchos reyes serán levantados desde los confines de la tierra.
“Duba! Ga sojoji suna zuwa daga arewa; babbar al’umma da sarakuna masu yawa suna tahowa daga iyakokin duniya.
42 Toman el arco y la lanza. Son crueles y no tienen piedad. Su voz ruge como el mar. Van a caballo, todo el mundo se pone en matriz, como un hombre a la batalla, contra ti, hija de Babilonia.
Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne marasa tausayi. Amonsu ya yi kamar rurin teku yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa kamar mutane a dāgār yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Babilon.
43 El rey de Babilonia ha oído las noticias de ellos, y sus manos se vuelven débiles. La angustia se ha apoderado de él, dolores como los de una mujer de parto.
Sarkin Babilon ya ji rahotanni game da su, hannunsa kuma ya yi laƙwas. Wahala ta kama shi, zafi kamar na mace mai naƙuda.
44 He aquí que el enemigo subirá como un león de la espesura del Jordán contra la fuerte morada; porque de repente haré que huyan de ella. Quienquiera que sea elegido, Lo nombraré por encima, porque ¿quién es como yo? ¿Quién me designará una hora? ¿Quién es el pastor que puede estar delante de mí?”
Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai dausayi, zan fafare Babilon daga ƙasan nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa domin wannan? Wane ne kamar ni da zai kalubalance ni? Kuma wanda makiyayi zai iya tsaya gāba da ni?”
45 Escucha, pues, el consejo de Yahvé que ha tomado contra Babilonia; y sus propósitos que se ha propuesto contra la tierra de los caldeos: Seguramente los arrastrarán, incluso a los pequeños del rebaño. Seguramente hará que su morada quede desolada sobre ellos.
Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Babilon, abin da ya nufa gāba da ƙasar Babiloniyawa. Za a kwashe ƙananan garkensu a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
46 La tierra tiembla por el ruido de la toma de Babilonia. El grito se escucha entre las naciones.
Da jin an ci Babilon da yaƙi sai duniya ta girgiza; za a ji kukanta cikin al’ummai.