< Jeremías 48 >

1 De Moab. Yahvé de los Ejércitos, el Dios de Israel, dice: “¡Ay de Nebo! Porque se ha desechado. Kiriathaim está decepcionado. Se toma. Misgab se pone en evidencia y se descomponen.
Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
2 La alabanza de Moab ya no existe. En Hesbón han ideado el mal contra ella: “¡Vamos! Dejemos de ser una nación’. Ustedes también, locos, serán llevados al silencio. La espada te perseguirá.
Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
3 El sonido de un grito de Horonaim, ¡desolación y gran destrucción!
Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
4 Moab es destruido. Sus pequeños han hecho que se escuche un grito.
Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
5 Porque subirán por la cuesta de Luhit con llanto continuo. Porque en el descenso de Horonaim han oído la angustia del grito de destrucción.
Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
6 ¡Huyan! ¡Salven sus vidas! Sé como el arbusto de enebro en el desierto.
Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
7 Pues, porque has confiado en tus obras y en tus tesoros, también será llevado. Chemosh saldrá en cautiverio, sus sacerdotes y sus príncipes juntos.
Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
8 El destructor vendrá sobre cada ciudad, y ninguna ciudad escapará; el valle también perecerá, y la llanura será destruida, como ha dicho Yahvé.
Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
9 Dale alas a Moab, para que pueda volar y alejarse: y sus ciudades se convertirán en una desolación, sin que nadie habite en ellas.
Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
10 “Maldito el que hace la obra de Yahvé con negligencia; y maldito el que aleja su espada de la sangre.
“La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
11 “Moab ha estado tranquilo desde su juventud, y se ha conformado con sus posos, y no se ha vaciado de buque a buque, ni ha ido al cautiverio; por lo que su gusto permanece en él, y su olor no se cambia.
“Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
12 Por lo tanto, he aquí que vienen los días”, dice Yahvé, “que enviaré a él a los que vierten, y se lo echarán; y vaciarán sus recipientes, y romper sus contenedores en pedazos.
Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
13 Moab se avergonzará de Chemosh, como la casa de Israel se avergonzó de Betel, su confianza.
Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
14 “¿Cómo decís: ‘Somos hombres poderosos, y hombres valientes para la guerra”?
“Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
15 Moab está asolado, y han subido a sus ciudades, y sus jóvenes elegidos han ido al matadero”. dice el Rey, cuyo nombre es Yahvé de los Ejércitos.
Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
16 “La calamidad de Moab está por llegar, y su aflicción se apresura.
“Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
17 Todos los que estáis a su alrededor, lamentadlo; y todos los que conocéis su nombre, decís, ‘Cómo se rompe el báculo fuerte, la hermosa vara”.
Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
18 “Tú, hija que habitas en Dibón, baja de tu gloria, y sentarse en la sed; porque el destructor de Moab ha subido contra ti. Ha destruido tus fortalezas.
“Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
19 Habitante de Aroer, quédate en el camino y observa. Pregúntale a él que huye, y a ella que escapa; decir: “¿Qué se ha hecho?
Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
20 Moab está decepcionado; ya que se descompone. ¡Llora y llora! Díganlo junto al Arnón, que Moab está asolado.
An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
21 El juicio ha llegado al país de la llanura... en Holon, en Jahzah, en Mephaath,
Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
22 en Dibon, en Nebo, en Beth Diblathaim,
zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
23 en Kiriathaim, en Beth Gamul, en Beth Meon,
zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
24 en Kerioth, en Bozrah, y sobre todas las ciudades de la tierra de Moab, lejanas o cercanas.
zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
25 El cuerno de Moab está cortado, y su brazo está roto”, dice Yahvé.
An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
26 “Embriágalo, porque se engrandeció contra Yahvé. Moab se revolcará en su vómito, y también será objeto de burla.
“Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
27 Pues, ¿no era Israel una burla para ti? ¿Se encontró entre ladrones? Ya que, por más que se hable de él, mueves la cabeza.
Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
28 Vosotros, habitantes de Moab, dejad las ciudades y habitad en la roca. Sé como la paloma que hace su nido sobre la boca del abismo.
Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
29 “Hemos oído hablar del orgullo de Moab. Es muy orgulloso en su altivez, su orgullo, su arrogancia, y la arrogancia de su corazón.
“Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
30 Yo conozco su ira — dice Yahvé —, que no es nada; sus fanfarronadas no han hecho nada.
Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
31 Por eso me lamentaré por Moab. Sí, gritaré por todo Moab. Estarán de luto por los hombres de Kir Heres.
Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
32 Con más que el llanto de Jazer Lloraré por ti, vid de Sibma. Sus ramas pasaron sobre el mar. Llegaron hasta el mar de Jazer. El destructor ha caído sobre tus frutos de verano y en su cosecha.
Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
33 La alegría y el gozo se alejan del campo fructífero y de la tierra de Moab. He hecho que el vino deje de salir de los lagares. Nadie pisará con gritos. El grito no será un grito.
Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
34 Desde el grito de Hesbón hasta Elealeh, incluso a Jahaz han emitido su voz, desde Zoar hasta Horonaim, hasta Eglath Shelishiyah; porque las aguas de Nimrim también se volverán desoladas.
“Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
35 Además, haré que cese en Moab”, dice Yahvé, “el que ofrece en el lugar alto, y al que quema incienso a sus dioses.
A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
36 Por eso mi corazón suena para Moab como las flautas, y mi corazón suena como flautas para los hombres de Kir Heres. Por lo tanto, la abundancia que ha conseguido ha perecido.
“Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
37 Porque toda cabeza es calva, y todas las barbas recortadas. Hay cortes en todas las manos, y un saco en la cintura.
An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
38 En todos los tejados de Moab, y en sus calles, hay lamentos por todas partes; porque he roto a Moab como una vasija en la que nadie se deleita”, dice Yahvé.
A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
39 “¡Cómo se rompe! ¡Cómo se lamentan! ¡Cómo Moab ha vuelto la espalda con vergüenza! Así que Moab se convertirá en una burla y un terror para todos los que le rodean”.
“Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
40 Porque Yahvé dice: “He aquí que volará como un águila, y extenderá sus alas contra Moab.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
41 Kerioth está tomada, y las fortalezas son tomadas. El corazón de los hombres poderosos de Moab en ese día será como el corazón de una mujer en sus dolores.
Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
42 Moab será destruido de ser un pueblo, porque se ha engrandecido contra Yahvé.
Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
43 El terror, la fosa y la trampa están sobre ti, habitante de Moab”, dice Yahvé.
Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
44 “El que huye del terror caerá en la fosa; y el que se levante de la fosa será tomado en la trampa, porque yo traeré sobre él, incluso sobre Moab, el año de su visita”, dice Yahvé.
“Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
45 “Los que huyeron se quedaron sin fuerzas bajo la sombra de Hesbón; porque el fuego ha salido de Hesbón, y una llama del medio de Sihon, y ha devorado el rincón de Moab, y la corona de la cabeza de los tumultuosos.
“A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
46 ¡Ay de ti, Moab! El pueblo de Chemosh está deshecho; porque tus hijos son llevados cautivos, y tus hijas en cautiverio.
Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
47 “Sin embargo, revertiré el cautiverio de Moab en los últimos días,” dice Yahvé. Hasta aquí el juicio de Moab.
“Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.

< Jeremías 48 >