< Jeremías 47 >

1 Palabra de Yahvé que vino al profeta Jeremías sobre los filisteos, antes de que el faraón atacara Gaza.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
2 Yahvé dice: “He aquí que las aguas suben del norte, y se convertirá en un arroyo desbordante, y desbordará la tierra y todo lo que hay en ella, la ciudad y los que la habitan. Los hombres llorarán, y todos los habitantes de la tierra se lamentarán.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
3 Al ruido del estampido de los cascos de sus fuertes, al correr de sus carros, al estruendo de sus ruedas, los padres no miran atrás por sus hijos porque sus manos son muy débiles,
da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
4 por el día que viene para destruir a todos los filisteos, para cortar de Tiro y de Sidón todo ayudante que quede; porque Yahvé destruirá a los filisteos, el remanente de la isla de Caphtor.
Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
5 La calvicie ha llegado a Gaza; Ashkelon es llevado a la nada. Tú, remanente de su valle, ¿cuánto tiempo te vas a cortar?
Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
6 “‘Espada de Yahvé, ¿cuánto tiempo pasará antes de que te calles? Vuelve a ponerte la vaina; Descansa y quédate quieto”.
“Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
7 “Cómo puedes estar tranquilo, ya que Yahvé te ha dado una orden? Contra Ashkelon, y contra la orilla del mar, allí lo ha designado”.
Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”

< Jeremías 47 >